’Yan ta’adda sun kashe sojoji 8 a wani hari a Borno

[ad_1]



Sojoji takwas sun rasa rayukansu yayin da wasu 23 suka jikkata bayan mayaƙan ISWAP suka kai hari wani sansanin soji a Jihar Borno.

Majiyoyin tsaro sun ce kusan mayaƙa 70 a kan babura ne suka kai harin a ƙauyen Cross Kauwa a ranar Litinin.

Rahotanni sun ce maharan sun taso daga sansani da ke wani tsibiri a Tafkin Chadi kafin su kai farmakin.

Sun ƙone wasu sassan sansanin, inda suka lalata wasu motocin soji tare da kwashe wasu makamai.

Sansanin yana da nisan kimanin kilomita 24 daga Baga, wani muhimmin gari da sansanin ke taimakawa wajen kare shi daga hare-haren ’yan ta’adda.

Harin na daga cikin waɗanda aka kai wa sansanonin soji a yankin Arewa Maso Gabas a baya-bayan nan.

Ƙungiyoyin ’yan ta’adda irin su ISWAP da Boko Haram na ci gaba da kai hare-hare duk da ƙoƙarin da jami’an tsaro ke yi.

Hukumomi sun ce sojoji da ’yan sa-kai na taimakawa wajen daƙile hare-hare a yankin.

Rikicin Boko Haram da ISWAP a Arewa Maso Gabas ya shafe sama da shekaru 10 ana yi.

A cewar Majalisar Ɗinkin Duniya, sama da mutane 40,000 ne suka rasa rayukansu yayin da kusan miliyan biyu suka rasa matsugunansu.

Rikicin ya kuma shafi maƙwabtan ƙasashe kamar Jamhuriyar Nijar, Chadi, da Kamaru.

A halin yanzu, Amurka ta tura sojojinta kusan 200 zuwa Najeriya domin bayar da horo da tallafin fasaha ga dakarun ƙasar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *