’Yan bindiga sun sanya dokar hana fita da harajin miliyan N30

[ad_1]



Mazauna ƙauyen Bilbis da ke ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara suna rayuwa ne cikin fargaba da takura, bayan da ’yan bindiga suka tilasta wa al’ummar garin shiga dokar hana fita daga gida har sai abin da hali ya yi.

Wannan ƙauye, wanda shi ne garin su Sanata mai wakiltar Zamfara ta Tsakiya, Ikira Aliyu Bilbis, ya zama fage na ƙunci da kukan neman agajin jin ƙai da kuma fuskantar fashi da makami.

A cewar wani mazaunin garin, Murtala Ahmed, ƙauyen ya shafe sama da kwanaki goma ƙarƙashin dokar hana fita ta tilas.

Ya bayyana cewa, duk wani mazaunin garin da aka gani a waje, ’yan ta’addan korarsa suke yi zuwa cikin gida, sannan su yi amfani da wannan damar wajen yin bincike a gidajen mutane don kwashe kaddarori da kuɗaɗe.

Lamarin ya ɗauki wani salo na daban kuma mai ban tsoro dab da fara watan Azumin Ramadan.

Bayan wani farmaki da dakarun soja suka kai kan shanun ’yan bindiga kusa da ƙauyen, ’yan ta’addan sun mayar da martani ta hanyar yanka dabbobin da suka ji rauni, sannan suka tilasta wa kowane gida siyan ƙananan sassan naman a kan kuɗi Naira 5,000 kowa ne gida.

Duk da haka, al’ummar garin suna fuskantar wani babban haraji na cin zarafi har Naira miliyan 30 da tawagar ta sanya musu.

Mazauna garin sun bayyana cewa tuni sun biya Naira miliyan 15 a matsayin yunƙuri na tsira da rayukansu don kauce wa zubar da jini.

A cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da ta karade shafukan sada zumunta zuwa ga Sanata Bilbis, mutanen da ke cikin firgici sun yi kukan halin rarrabuwar kawuna da ake ciki, inda suka lura cewa mazauna garin da yawa suna cikin talauci har ma ba za su iya biyan kuɗin mota don tserewa zuwa wurare masu aminci kamar Gusau ba.

A martanin da ta mayar kan wannan rikicin da ke ƙaruwa, Rundunar ’Yan Sandan Jihar ta sanar da cewa, wata haɗaɗɗiyar rundunar haɗin gwiwa ta soja da ’yan sanda ta yi nasarar sake buɗe hanyoyin Kucheri zuwa Bilbis zuwa da Danjibga zuwa Keta.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya tabbatar da cewa rukunin ƙwararru kan kwance bama-bamai (EOD) sun gano tare da lalata bama-baman da aka binne a ƙasa (IEDs) da ‘yan ta’addan suka dasa don tare hanyar samar da abinci da zirga-zirga.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *