Madrid Da PSG Na Shirin Sayen Osimhen
[ad_1]
Kungiyoyin Real Madrid da PSG na sa ido kan Victor Osimhen, yayin da ake hasashen yiwuwar sayensa a kasuwar bazara.
A cewar dan jaridar Turkiyya Ali Naci Küçük, Real Madrid ta sanya Osimhen da Erling Haaland na Manchester City cikin jerin zabin ‘yan wasan da take son dauka a kakar wasa mai zuwa.
Küçük ya kara da cewa wakilan Real Madrid da PSG sun halarci filin wasa na Rams Park a ranar Talata da ta gabata domin kallon Osimhen yayin wasan Galatasaray a gasar UEFA da Liverpool FC.
Real Madrid ta dade tana bibiyar Osimhen, kuma a halin da kwangilar wasu ‘yan wasanta ke ciki—musamman Vinícius Júnior—na kara yiwuwar tabbatar wannan ciniki.
[ad_2]
Source link