Madrid Da PSG Na Shirin Sayen Osimhen

[ad_1]

Kungiyoyin Real Madrid da PSG na sa ido kan Victor Osimhen, yayin da ake hasashen yiwuwar sayensa a kasuwar bazara.

A cewar dan jaridar Turkiyya Ali Naci Küçük, Real Madrid ta sanya Osimhen da Erling Haaland na Manchester City cikin jerin zabin ‘yan wasan da take son dauka a kakar wasa mai zuwa.

Küçük ya kara da cewa wakilan Real Madrid da PSG sun halarci filin wasa na Rams Park a ranar Talata da ta gabata domin kallon Osimhen yayin wasan Galatasaray a gasar UEFA da Liverpool FC.

Real Madrid ta dade tana bibiyar Osimhen, kuma a halin da kwangilar wasu ‘yan wasanta ke ciki—musamman Vinícius Júnior—na kara yiwuwar tabbatar wannan ciniki.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *