Tinubu Ya Miƙa Sunan Taiwo Oyedele A Matsayin Ƙaramin Ministan Kuɗi

[ad_1]

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya miƙa sunan Taiwo Oyedele domin naɗa shi a matsayin ƙaramin ministan kuɗi.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce an aika sunan Oyedele zuwa Majalisar Dattawa domin tantance shi ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio.

  • Yaƙin Iran Zai Asassa Tashin Farashin Man Fetur A Nijeriya
  • Ronaldo Ya Fice Daga Saudi Arabia Yayinda Hare-Haren Kasar Iran Suka Zafafa

Oyedele zai maye gurbin Doris Uzoka-Anite.

Ita kuma an mayar da ita Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa a matsayin Ministar Ƙasa.

Wannan shi ne muƙaminta na uku a wannan gwamnati.

Wane ne Taiwo Oyedele?

Oyedele ƙwararre ne a fannin tattara haraji, kuma masanin tattalin arziƙi da lissafi ne.

Ya taɓa zama shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Tsarin Haraji.

Ya yi aiki na shekaru da dama a kamfanin Price water house Coopers (PwC), inda ya kasance jagora a harkar haraji a Afirka.

Ya yi karatu a Yaba College of Technology, sannan ya samu digiri daga Oxford Brookes University.

Haka kuma ya halarci manyan shirye-shiryen a Harvard Kennedy School da sauran manyan makarantu.

Oyedele na daga cikin waɗanda suka jagoranci tsara sabbin dokokin haraji a Nijeriya.

An amince da dokokin ne bayan muhawara mai tsawo a Majalisar Tarayya, sannan Shugaba Tinubu ya rattaba musu hannu a watan Yunin 2025.

Dokokin sun fara aiki a ranar 1 ga watan Janairu, 2026.

Ana sa ran naɗinsa zai ƙara ƙarfafa gyaran tsarin haraji da ƙara samun kuɗaɗen shiga ga gwamnati tare da bunƙasa zuba jari a ƙasar.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *