Tinubu Ya Miƙa Sunan Taiwo Oyedele A Matsayin Ƙaramin Ministan Kuɗi
[ad_1]
Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya miƙa sunan Taiwo Oyedele domin naɗa shi a matsayin ƙaramin ministan kuɗi.
Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce an aika sunan Oyedele zuwa Majalisar Dattawa domin tantance shi ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio.
- Yaƙin Iran Zai Asassa Tashin Farashin Man Fetur A Nijeriya
- Ronaldo Ya Fice Daga Saudi Arabia Yayinda Hare-Haren Kasar Iran Suka Zafafa
Oyedele zai maye gurbin Doris Uzoka-Anite.
Ita kuma an mayar da ita Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa a matsayin Ministar Ƙasa.
Wannan shi ne muƙaminta na uku a wannan gwamnati.
Wane ne Taiwo Oyedele?
Oyedele ƙwararre ne a fannin tattara haraji, kuma masanin tattalin arziƙi da lissafi ne.
Ya taɓa zama shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Tsarin Haraji.
Ya yi aiki na shekaru da dama a kamfanin Price water house Coopers (PwC), inda ya kasance jagora a harkar haraji a Afirka.
Ya yi karatu a Yaba College of Technology, sannan ya samu digiri daga Oxford Brookes University.
Haka kuma ya halarci manyan shirye-shiryen a Harvard Kennedy School da sauran manyan makarantu.
Oyedele na daga cikin waɗanda suka jagoranci tsara sabbin dokokin haraji a Nijeriya.
An amince da dokokin ne bayan muhawara mai tsawo a Majalisar Tarayya, sannan Shugaba Tinubu ya rattaba musu hannu a watan Yunin 2025.
Dokokin sun fara aiki a ranar 1 ga watan Janairu, 2026.
Ana sa ran naɗinsa zai ƙara ƙarfafa gyaran tsarin haraji da ƙara samun kuɗaɗen shiga ga gwamnati tare da bunƙasa zuba jari a ƙasar.
[ad_2]
Source link