Super Falcons ta samu gurbin buga Kofin Afrika
[ad_1]
Babbar tawagar ƙwallon ƙafa ta matan Najeriya Super Falcons ta samu tikitin buga gasar cin kofin nahiyyar Afrika ta mata ta 2026 da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci.
Super Falcons ta samu nasarar ne bayan tashi kunnen doki 1 da 1 da takwararta ta jamhuriyyar Benin a filin wasa na MKO Abiola da ke birnin Abeokuta a yammacin jiya Talata.
Kunnen doki ya bai wa Najeriya nasarar shiga cikin jerin ƙasashen da zasu buga kofin na Afrika, bayan Falcons ta doke Benin da ci 2 – 0 a makon jiya a birnin Cotonou.
Hakan na nufin a wasanni biyu da ƙungiyyoyi suka fafata Najeriya ta samu nasara da ci 3-1.
Wannan dai shi ne karo na 14 da Falcons zata buga kofin nahiyyar Afrika da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci daga 17 ga watan Maris zuwa 3 ga watan Afrilu na 2026.
Najeriya ta lashe gasar sau 10 cikin gasanni 14 da aka buga a tarihi.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link