Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali

[ad_1]



Rahotanni daga sojojin da ke mulki a Mali, sun ce sun kama wasu sojoji kusan 30 da ake zargin suna shirin kifar da gwamnati ƙasar.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa cikin waɗanda aka kama akwai Janar Abass Dembele, tsohon gwamnan yankin Mopti da ke tsakiyar ƙasar.

Har yanzu gwamnatin ƙasar ba ta fitar da sanarwa a hukumance ba game da lamarin.

Ita ma gwamnatin da ke mulki yanzu ta karɓi mulki ne ta hanyar juyin mulki a shekarar 2021.

Wannan zargi ya ƙara nuna cewa akwai rashin kwanciyar hankali a tsakanin gwamnatin sojin.

Yanzu haka dai gwamnatin na fuskantar matsalar hare-haren masu iƙirarin jihadi a Arewacin Mali.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *