Sai ranar Asabar za a yi Sallah a Iran

[ad_1]



Gwamnatin Iran ta sanar da cewa sai a gobe Asabar ce za a gudanar da Idin Sallah ƙarama a ƙasar da mafi rinjayen musulmanta mabiya shi’a ne.

A cewar gidan talabijin na ƙasar, ofishin jagoran addini na Iran, Mojtaba Khamenei, ya bayyana cewa yau Juma’a ce za ta kasance rana ta 30 ga watan Ramadan bayan hukuncin da masu duban wata na ƙasar suka tabbatar.

Sanarwar ta kuma yi daidai da ta ƙasar Iraƙi, inda babban malamin Shi’a, Ayatollah Ali al-Sistani, ya amince da Asabar a matsayin ranar sallah.

A bana, ƙarshen watan Ramadan a ƙasar ya zo daidai da bikin Nowruz, wato sabuwar shekarar gargajiya da ake yi a Iran.

Ana tantance ranar Sallah ne bisa ganin jinjirin wata kamar yadda tsarin kalandar Musulunci ya tanada, yayin da ake gudanar da azumi wanda ke daga cikin rukunan addinin Musulunci.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *