Rikicin Wike Da Fubara Na Ƙara Tsananta, Tinubu Ya Sake Shiga Tsakani
[ad_1]
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake tsoma baki a rikicin siyasa da ke ci gaba da gudana tsakanin Gwamnan Jihar Ribas Siminalayi Fubara, da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike. Majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa Tinubu ya gayyaci Wike zuwa wani muhimmin taro a ƙasashen waje domin shawo kan sabon rikicin da ya sake ɓarkewa a a jihar mai arzikin man fetur.
Rahotanni sun nuna cewa ana sa ran taron zai gudana ne a birnin Dubai na ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), bayan Shugaban Ƙasa ya kammala wata gajeriyar ziyarar aiki a Faransa. Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta ce Tinubu na kallon matakan da Wike ke ɗauka a matsayin barazana ga zaman lafiya a yankin Neja-Delta, tare da jaddada cewa ba za a amince da duk wani yunƙurin tsige Gwamna Fubara ba.
- Sakataren APC Ya Buƙaci Murabus Ɗin Wike Saboda “Tsoma Baki” A Harkokin Jam’iyya
- Jam’iyyar APC Ta Ribas Ta Yi Watsi Da Matakin Tsige Gwamna Fubara
Rikicin ya ƙara tsananta ne bayan ƴan majalisar dokokin Jihar Rivers 27, waɗanda ake ganin suna goyon bayan Wike, suka ƙaddamar da sabon yunƙurin tsige Gwamna Fubara da mataimakiyarsa, Farfesa Ngozi Odu. An zargi gwamnan da manyan laifuka kamar rusa ginin majalisa, da kashe kuɗaɗe ba tare da kasafi ba, da kuma bijirewa hukuncin Kotun Ƙoli kan ikon kuɗaɗen majalisa, yayin da aka zargi mataimakiyar gwamnan da almubazzaranci da toshe ayyukan majalisa.
Duk da ƙoƙarin sasanci da Tinubu ya yi a baya, zaman lafiyar da aka samu na wucin gadi ya rushe bayan watanni kaɗan. Rikicin ya sake ɗaukar sabon salo da zargin cin amana da kalaman siyasa masu zafi, lamarin da ya jawo kira daga manyan ‘yan siyasa da jam’iyyar APC na ƙasa da ƙasa da a sake sasantawa domin kare zaman lafiya, da tsaro da martabar Shugaban Ƙasa, tare da hana rikicin haifar da tangarɗa ga tattalin arziƙi da tsaron ƙasa.
[ad_2]
Source link