Ranar Mata Ta Duniya: Mata Kashi 60 A NPA Ke Rike Da Mukamai Na Musamman —Dantsoho
[ad_1]
Shugaban Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya sanar da cewa, Hukumar ba ta mayar da mata saniyar ware ba, domin kuwa, kaso 60 a cikin dari na matan da ke aiki a Hukumar, na rike da mukaman Mataimakin Injiniya.
Wannan furucin na Dantsoho, na zuwa ne, a yayin da aka gudanar da zagowar bikin ranar mata duniya, da aka saba gudanarwa a duk ranar 8 na kowanne watan Maris na na kowacce shekara.
- Yawan Dazuzzuka Da Filin Ciyayi a Kasar Sin Ya Wuce Kashi 56%
- Sin Ta Himmatu Wajen Raya Ci Gaban Duniya Na Bai Daya
Shugaban ya bayyana cewa, wannan matakin na nuna cewa, Hukumar ba ta kyamar mata kuma tana janyo su a Niki, domin su ma ayi tafiya da su, yadda sima za su bayar da ta su gudunmawar, wajen kara ciyar da kasar gaba.
Dantsoho ya bayyana haka a jawabinsa a taron bikin zagayowar ranar, musamman ga matan da ke yin aiki, a Hukumar.
A cewarsa, nade-naden mukamai da aka yiwa matan da ke aiki a Hukumar, na daga cikin matakan kara ba su damar gudanar da shugabanci, a Hukumar.
“Mata na rike da mukamai da suka kai kaso 60 a cikin dari a Hukumar ta NPA, inda kuma maza ke rike da mukamai kaso 40 a cikin dari, a Hukumar,” Inji Dantsoho.
Ya kara da cewa, wadannan matakan sun nuna a zahiri irin, mayar da hankali da Hukumar ta ke ci gaba da yi, na bai wa mata damar samun cin nasara a fannin na sufurin Jiragen Ruwa na kasar nyi, hakan ya nuna cewa, Mad’s da ke aiki a Hukumar, ba su iya mama ye ayyukan Hukumar ba…
Shugaban na Hukumar ta NPA ya jinhinawa matan da ke aiki a Hukumar musamman kan gudunmawar da su ke ci gaba da bayarwa, a sassa da ban da ban na Hukumar.
Shugaban ya bayyana cewa, matan da ke aiki a Hukumar na kara samun daukaka wajen gudanar da ayyukan su tare da kuma yin aiki da kwarwa, a bangaren gudanar da harkar mulki, a Hukumar.
Dantsoho ya sanar da cewa, karuwar gudunmawar da matan da ke aiki a Hukumar ke ci gaba da yi, hakan ya sanya maza ‘yan uwansu, ba su iya mamaye daukacin ayyukan da ake gudanarwa a Hukumar ba.
[ad_2]
Source link