Pakistan ta ƙaddamar munanan hare-hare kan Afghanistan
[ad_1]
A wannan Lahadin ce Pakistan ta bayyana cewa ta kai wasu jerin hare-hare ta sama kan ’yan bindiga a maƙwabciyarta Afghanistan.
Sai dai hukumomin Afghanistan sun ce yara na daga cikin ɗaruruwan fararen hula da suka mutu ko suka jikkata.
Hare-haren da aka kai cikin dare su ne mafi girma tun bayan gumurzun kan iyaka na watan Oktoban bara da ya kashe sama da mutum 70 a ɓangarorin biyu tare da jikkata ɗaruruwa.
A cewar Islamabad, an kai hare-haren ne kan wurare bakwai a yankunan da ke kan iyaka, domin a cewarta, mayaƙan da ke Afghanistan ne ke da alhakin hare-haren ƙunar baƙin wake da suka faru kwanan nan a Pakistan.
Wata sanarwa daga Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Pakistan ta ce sojoji sun kai farmaki kan mayaƙan Taliban na Pakistan da abokan aikinsu, da kuma wani reshen ƙungiyar IS.
Sai dai Ma’aikatar Tsaron Afghanistan ta ce “ɗaruruwan fararen hula da ba su ji ba kuma ba su gani ba, ciki har da mata da yara, sun mutu ko sun jikkata” bayan da hare-haren suka afka kan wata makarantar allo da gidaje a lardunan Nangarhar da Paktika.
Wani ɗan jaridar AFP da ke gundumar Bihsud a Nangarhar ya ce mazauna yankin, wanda ke da tsaunuka da keɓantacce, sun haɗa kai da masu ceto domin tono mutane daga ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine, suna amfani da injina da fatake.
“Mutanen nan talakawa ne. Mazaunan ƙauyen nan ‘yan uwanmu ne. Lokacin da bam ya faɗi, wani da ya tsira yana ihu yana neman taimako,” in ji wani mutum, Amin Gul Amin, mai shekaru 37.
‘Yan sanda a Nangarhar sun shaida wa AFP cewa harin ya fara ne kusan tsakar dare, inda ya shafi gundumomi uku.
“Fararen hula sun mutu. A wani gida akwai mutum 23; an fitar da mutum biyar da suka jikkata,” in ji kakakin ‘yan sanda, Sayed Tayeeb Hammad.
“Za mu mayar da martani”
Ma’aikatar Tsaron Afghanistan ta ce za ta mayar da “martanin da ya dace kuma a tsanake” kan hare-haren Pakistan.
Tun bayan da Taliban suka sake karɓar iko da Afghanistan a 2021, alaƙar ƙasashen biyu ta ƙara tsami.
Wani rahoton Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce hare-haren sojojin Pakistan sun kashe fararen hula Afghan 70 tsakanin Oktoba da Disamba.
An taɓa gabatar da shawarwari da dama bayan tsagaita wuta da Qatar da Turkiyya suka shiga tsakani, amma ba a cimma yarjejeniya mai ɗorewa ba.
A wannan watan, Saudiyya ta shiga tsakani wajen sasanta sakin sojojin Pakistan uku da Afghanistan ta kama a Oktoba.
Rikicin ya shafi rayuwar jama’a a ɓangarorin biyu, inda aka rufe iyakar ƙasa tsawon watanni.
Pakistan ta ce duk da roƙon da ta yi, Taliban ba su ɗauki matakin da ya dace kan ‘yan bindigar da ke amfani da ƙasar Afghanistan wajen kai hare-hare a Pakistan ba, zargin da gwamnatin Afghanistan ta musanta.
An kai hare-haren ne bayan fashewar bam a masallacin ‘yan Shi’a da ke Islamabad makonni biyu da suka gabata, da kuma wasu hare-hare a arewa maso yammacin Pakistan.
Ƙungiyar IS ta ɗauki alhakin harin masallacin da ya kashe aƙalla mutum 40 tare da jikkata sama da 160, wanda shi ne mafi muni a Islamabad tun 2008.
Haka kuma, reshen ƙungiyar IS a yankin Khorasan, ya ɗauki alhakin wani harin ƙunar baƙin wake a wani gidan cin abinci a Kabul a watan da ya gabata.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link