NCoS Ta Kama Mutane 2 Bisa Yunƙurin Safarar Miyagun Ƙwayoyi Zuwa Gidan Yarin Kano

[ad_1]

Jami’an Hukumar kula da gidajen yarin Nijeriya, NCoS, a jihar Kano, ta kama mutane biyu bisa zargin yunkurin safarar wiwi da sauran miyagun kwayoyi zuwa ga fursunoni a harabar matsalaicin gidan yarin da ke Kano.
Wannan yana kunshe ne a cikin wata sanarwa da Kakakin Hukumar a Kano, CSC Musbahu Lawan Kofar nasarawa ya fitar a ranar Laraba a Kano.
Ya ce wadanda ake zargin, Usman Khalid, mai shekaru 25, da Bello Musa Ahmed, mai shekaru 24, dukkansu mazauna yankin Tsamiya (Birget) ta jihar, jami’an hukumar da ke aiki a matsakaiciyar cibiyar ta Goron Dutse ne suka kama su.
A cewarsa, an kama wadanda ake zargin ne yayin da ake zarginsu da yunkurin jefa wiwi da sauran muggan kwayoyi ga fursunoni a harabar cibiyar.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *