Majalisar Jihar Ribas Ta Dakatar da Shirin Tsige Gwamnan Fubara
[ad_1]
Majalisar Dokokin Jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Gwamna Siminalayi Fubara da Mataimakiyarsa, Ngozi Odu, bayan sa bakin da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi a lamarin.
An amince da matakin dakatarwar ne a zaman majalisar da aka koma a ranar Alhamis a Fatakwal, babban birnin jihar. Wannan na zuwa ne bayan majalisar ta fara shirin tsige su a zamanta na farko na shekarar 2026 kan zargin aikata manyan laifuka.
- HOTUNA: Wike Ya Buɗe Gidan Rediyo Don Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu A Ribas
- Fubara Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Ribas
Daga cikin zarge-zargen da aka ambata akwai rushe ginin majalisar dokokin jihar da kuma kashe kuɗi ba tare da amincewar majalisa ba, da sauran batutuwa.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a fitar da cikakken bayani kan dalilan dakatar da shirin tsigen ba.
[ad_2]
Source link