Hatsarin mota ya jikkata mutane da dama a Filato

[ad_1]



Fasinjoji da dama sun samu raunuka a safiyar ranar Alhamis bayan da wata motar bas ta Sharon ta yi karo da wata motar bas mai mutane 18 ta jami’ar Jos, a hanyar Kwanan Randa da ke Jibam a ƙaramar hukumar Pankshin ta Jihar Filato.

Wasu majiyoyi daga al’ummar yankin sun shaida wa Wakilinmu cewa, motar bas da ke wannan cibiyar tana kuma da rubutu a jikinta na  ƙungiyar wasannin jami’o’in Najeriya (NUGA).

Wani ganau mai suna Dimka Nenrit, wanda ya zanta da wakilinmu, ya ce motar bas mai mutane 18 na tafiya zuwa Dabat da ke ƙaramar hukumar Qua’anpan domin halartar binne gawa a lokacin da hatsarin ya afku.

Ya bayyana hatsarin a matsayin mai muni, yana mai jaddada cewa kusan dukkan mutanen da ke cikin motocin biyu sun samu raunuka daban-daban. Ba tare da ɓata lokaci ba, aka kai waɗanda suka jikkata zuwa wani asibitin da ke kusa domin samun kulawar gaggawa. “Muna godiya ga Allah da ba a samu asarar rai ba a lokacin ceto mutanen ba,” in ji shi.

“Hatsarin da  ya afku ya kawo ruɗani  yayin da masu tausayawa, masu aikin sa kai na al’umma, da masu ba da agajin gaggawa suka yi ta ƙoƙarin kuɓutar da waɗanda hatsarin ya rutsa da su tare da cire tarkacen da suka rufe hanyar.

Hatsarin ya haifar da cunkoson ababen hawa a kan titin mai cike da cunkoson jama’a, lamarin da ya sa masu ababen hawa suka maƙale na sa’o’i da dama kafin masu aikin sa kai da jami’an tsaro su warware hanyar tare da dawo da zirga-zigar ababen hawa,” in ji shi.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *