Hukumar Yaƙi Da Masu Safarar Mutane Ta Ceto Mutum 17 A Nasarawa
[ad_1]
Rundunar ’Yansandan Jihar Nasarawa ta samu gagarumar nasara a ƙoƙarinta na yaƙi da laifuka, bayan ceto mutane 17 da ake zarginsu da laifin safarar mutane.
Kakakin Rundunar ’Yansandan jihar, SP Ramhan Nansel, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Lafia, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar, an ceto mutanen ne a ranar Asabar da misalin ƙarfe 5:50 na yamma, lokacin da jami’an sintiri da ke ƙarƙashin sashen ’Yansanda na Mararaba “A” suka tare wata farar mota ƙirar Volkswagen Sharon mai lambar rajista SHD 253 YU, a yayin wani aikin tsayawa da bincike a Sharp Corner da ke Ƙaramar Hukumar Karu ta jihar.
- NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya
- An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane
Nansel ya ce motar na hannun wani Nanle John, mai shekaru 36, kuma tana ɗauke da fasinjoji 17, samari 11 da kuma ƴammata da shida, masu shekaru tsakanin 10 zuwa 19.
“Bayan yi musu tambayoyi, an fara zargin cewa fasinjojin waɗanda aka ceto suna iya kasancewa waɗanda aka yi safarar su ne. Ƙarin bincike ya nuna cewa direban da fasinjojin sun bayyana cewa suna tafiya ne daga Shendam a Jihar Filato zuwa Kayama a Jihar Kwara domin haɗuwa da wani Umaru (da ba a san sunan babansa ba), wanda ake zargin ya ruɗe su tare da yi musu alƙawarin samar musu da ayyukan noma a garin Kayama,” in ji shi.
[ad_2]
Source link