HOTUNA: Yadda Musulmi ke gudanar da bikin Sallah Ƙarama

[ad_1]



A yau Juma’a, 20 ga watan Maris ne musulmi a sassan daban-daban na duniya ke gudanar da bikin sallah ƙarama ko kuma Idu-al-Fitr bayan kammala azumi 30 na watan Ramadan.

Sai dai tun a jiya Alhamis, wasu ƙasashe da yankuna sun gudanar da tasu sallar bayan sanar da ganin jinjirin watan Shawwal tun a ranar Laraba.

Galibi akan samu banbancin ranakun gudanar da sallar daga ƙasa zuwa ƙasa ko kuma daga wani yanki zuwa wani, kamar yadda ya faru a bana, inda ko a Najeriya duk da sanarwar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar ta rashin ganin jinjirin watan a ranar Laraba, wasu yankuna kamar a Jihar Sokoto sun gudanar da sallar Idi a jiya Alhamis.

Kazalika, a Jamhuriyyar Nijar ma an gudanar da bikin sallar bayan ganin jinjirin watan Shawwal tun a ranar Laraba, kodayake akwai wasu tsiraru da sai a yau ne suka gudanar da nasu bikin sallar bayan saukowa daga Idi.

Yadda aka yi Sallar Idi a Babban Masallacin reshen sabuwar Jami’ar Bayero da ke Kano.

📸: Abubakar Muhammad


Hotuna daga Masallacin Idin Apo da ke Abuja

📸: Onyekachukwu Obi


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *