HOTUNA: Yadda fararen hula ke ficewa daga Lebanon saboda hare-haren Isra’ila

[ad_1]



A yayin da Isra’ila ke zafafa hare-haren kan Lebanon ciki har da birnin Beirut, tuni fararen hula suka soma ficewa domin neman mafaka.

Hare-haren bama-bamai da aka kai a kudanci da gabashin Lebanon, da kuma unguwannin kudancin birnin Beirut, sun tilasta wa fiye da mutane 28,500 barin muhallansu, a cewar hukumar kula da bala’o’i da bayar da agajin gaggawa ta gwamnati.

Lamarin na zuwa ne bayan da Hezbollah wadda tuni gwamnatin Lebanon ta haramta ayyukanta, ta harba rokoki da jirage marasa matuƙa zuwa Isra’ila a mastayin fansar kai wa Iran hari.

Hoton wasu iyalai da ke tsere wa harin Isra’ila a Kudancin Lebanon Hoto: AP
Wasu iyalai da suka yada zango a yankin Dahiyeh da ke Kudancin Beirut Hoto: AP
Wata yarinya ke nan bayan isowar motarsu Kudancin garin Sidon domin neman mafaka Hoto: AP


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *