Gwamnatin Tarayya Ta Soke Bikin Faretin Ranar Samun ’Yancin Kai

[ad_1]

Gwamnatin Tarayya ta soke faretin da aka shirya yi don bikin cikar Nijeriya shekara 65 da samun ’yancin kai a ranar Laraba, 1 ga watan Oktoba, 2025.

A wata sanarwa daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, ya ce an ce sokewar ba ta za ta rage muhimmancin wannan rana ba.

Segun Imohiosen, Daraktan Hulɗa da Jama’a, ya ce sauran shirye-shiryen bikin za su gudana kamar yadda aka tsara.

Gwamnati ta nemi afuwa kan duk wata matsala da wannan mataki zai iya jawo wa ’yan ƙasa.

Haka kuma ta roƙi ’yan Nijeriya su ci gaba da goyon bayan tsare-tsaren Shugaba Bola Tinubu, tana mai tabbatar da cewa gwamnati na ƙoƙarin gina Nijeriya.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *