Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

[ad_1]


Majalisar zartaswar jihar Jigawa ta amince da fitar da naira biliyan 2.5 don nazarin yanayin kasa domin gano yuwuwar samun makamashin Uranium, ɗanyen mai da iskar gas a cikin jihar.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na Jihar, Hon. Sagir Musa ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan taron majalisar zartarwar jihar a ranar Laraba.

Ya bayyana cewa, amincewa da binciken a wasu keɓantattun wurare, ya biyo bayan karatun share fage na shekaru da rahotanni kan albarkatun ma’adanai daban-daban a fadin jihar Jigawa.

Hon. Musa ya kara da cewa, aikin zai mayar da hankali ne kan nazari da binciken kimiyyar kasa a yankunan da ake tunanin cewa suna dauke da uranium, danyen man fetur, da iskar gas, da nufin tattara dukkan bayanan da ake bukata don ci gaba da aiki.

A cewar kwamishinan, amincewar wani bangare ne na manufofin gwamnatin Gwamna Umar Namadi na binciko albarkatun ma’adanai na jihar don haɓaka tattalin arzikin cikin gida mai ɗorewa.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *