Gwamnan Sakkwato Ya Mayar Da Malaman Islamiyya Ma’aikata Ya Rabawa Mahaddata Babura
[ad_1]
Gwamnan Jihar Sakkwato Ahmed Aliyu ya bayar da umurnin daukar malaman makarantar Ma’ahadut Tahfizi Waddarasatul Qur’aniyya 53 aiki a matsayin ma’aikatan gwamnatin jiha nan take.
Gwamnan ya umurci ma’aikatar lamurran addini da ta hada hannu da ma’aikatar kudi domin tabbatar da saka malaman a cikin tsarin albashi daga watan maris.
Haka ma gwamnatin ta bayar da kyautar babura 259 ga daliban da suka haddace Alkur’ani a bikin yaye mahaddatan.
A cewar Gwamnan ba wai suna murnar kammala haddar Alqur’anin daliban ba ne kawai ba suna kuma murnar sadaukarwa, jajircewa ladabi da biyayya da himmatuwa ga koyarwar ubangiji.
[ad_2]
Source link