Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba Ɗaya

[ad_1]

Gwamnan Neja, Mohammed Umaru Bago, ya sallami dukkan mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar.

Gwamnan ya bayyana labari sallamar ta su ne a taron majalisar da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Minna, babban birnin jihar, da safiyar yau Litinin 1 ga Satumbar 2025

Ya gode wa mambobin majalisar bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar, tare da yi musu fatan alheri a duk inda makomar aiki ta kai su.

Sai dai, gwamnan ya bayyana cewa ya bar Sakataren Gwamnatin Jihar, da Shugaban Ma’aikatansa da kuma Mataimakinsa da wasu manyan jami’an ofishinsa a muƙamansu.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *