Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
[ad_1]
Hukumar Tattara Haraji ta Ƙasa (FIRS) ta ce ma’aikatanta hudu sun mutu a gobarar da ta tashi a ginin Afriland Towers da ke titin Broad da ke Legas, a ranar Talata.
Aminiya ta rawaito yadda gobara ta mamaye ginin da ke dauke da banki, hukumomi da wasu kamfanoni.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Laraba, mai magana da yawun Shugaban FIRS, Zaach Adedeji, wato Dare Adekanmbi, ya ce hukumar na cikin jimami da alhini kan rasuwar ma’aikatan nata.
Sanarwar ta ce, “Cike da alhini da bakin ciki, FIRS na sanar da rasuwar ma’aikatanta hudu a gobarar da ta tashi a ginin Afriland Towers da ke titin Broad, Legas, a ranar Talata. FIRS na daya daga cikin masu haya a ginin, inda Ofishin Binciken Matsakaicin Haraji da Ofishin Haraji na Onikan ke a bene na shida da na bakwai.”
“Jami’an tsaro da na kula da lafiya na hukumar sun gaggauta tuntubar hukumar kashe gobara lokacin da aka sanar da su. Amma da suka isa wurin, hayaki mai kauri da duhu ya turnuke ginin.”
“Hukumar da dukkan ma’aikatanta na cikin alhini kan wannan lamari. Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka rasu, kuma muna tare da su a wannan lokaci mai wahala. Za mu ba su dukkan goyon baya da tallafi da ake bukata.”
“Muna aiki tare da dukkan hukumomin da suka dace a Legas domin gano musabbabin wannan mummunan al’amari. A yayin da ake ci gaba da bincike, za mu duba matakan kiyaye lafiyar dukkan ofisoshin FIRS da ke fadin ƙasa, ko na haya ne ko wanda ta mallaka.”
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link