Champions League: Real Madrid ta lallasa Man City a Santiago

[ad_1]



Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta doke Manchester City da ci uku da nema a filin wasa na Santiago Bernabeau da ke birnin Madrid.

Ƙungiyoyin biyu sun fatata a wasan zagayen ’yan 16 na Gasar Zakarun Turai (UEFA Champions League) a daren ranar Laraba.

Sai dai wasan bai yi wa baƙi daɗi ba, domin Madrid ta yi musu wankan jego mai zafin gaske.

Ɗan wasan tsakiyar Real Madrid, Fede Verlvade ne ya jefa wa Manchester City ƙwallo uku rigis a ragarta.

Ɗan wasan ya fara jefa ƙwallo a minti na 20 da minti na 27, sannan ya ƙarƙare a wata ƙwallon a minti na 42.

Hakazalika ɗan wasa Vinicius Jrn ya samu bugun fenariti a minti na 57, amma mai tsaron ragar Manchester City, Donnaruma ya tare ƙwallon.

Yanzu dai ƙungiyoyin za su sake fafatawa da juna a ranar Talata mai zuwa a filin Etihad da ke Ingila, domin ware wanda zai je mataki na gaba na gasar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *