Category: Latest News

  • Majalisun Dokokin Jihohi Sun Goyi Bayan Kafa ‘Yansandan Jiha

    [ad_1]

    Shugabannin majalisun Jiohi a karkashin, kungiyar shugabannin majalisun Nijeriya (CSSLN), sun ba da nasu goyon bayan dangane da lamarin kirkirar ‘yansandan Jiha.

    Sun bayyana cewa maganar kafa ‘yansandan jiha, ai tun tuni ne ya dace ace an kafa ta saboda yadda lamarin tababarewar tsaro yake a fadin Nijeriya, don haka  ya ce, ba abu ne maikyau ace an ki amincewa da shawarar yin hakan.

    • An Yi Musayar Kwarewa Game Da Ayyukan Rage Talauci Ga Masu Bukatar Musamman Na Sin a Dandalin FAO
    • Za a Gudanar Da Tattaunawa Kan Batun Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka a Faransa Daga Ranar 14 Zuwa 17 Ga Watan Maris

    Maganar kafa ‘yansandan jihar makon da ya gabata ta kara samun tagomashi yayin da sabon Shugaban rundunar ‘yansanda ta kasa, wanda aka rantsar makon da ya gabata, Tunji Disu, ya ba da  tashi amincewar inda ya kafa kwamitoci domin   su gano hanyoyin da za’a bi na kafa su.

    Disu, wanda ya  yi hira  ne da masu daukar labaranfadar Shugaban kasa jim kadan bayan da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da shi a matsayin Shugaban rundunar ‘yansanda na 23 a fadar Shugaban kasa,  ya ce maganar samar da ‘yansandan Jihohi wani abu ne da za a iya kira da “tsari ne wanda lokacin shi ya yi.”

    Kafin dai a samu zuwa wannan lokacin da halin da ake ciki, Tinubu ya yi kira da majalisun kasa su ba lamarin taimako na shari’a.

    An samu mabambanta ra’ayoyi akan maganar da sabon Shugaban rundunar ‘yansanda ta kasa ya yi. Kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF), Afenifere, da takwarar ta, ta kudu maso kudu, da kungiyar sashen masu arzikin manfetur (Pan Niger Delta Forum), sun goyi bayan lamarin na ‘yansandan Jiha.

    Duk da yake dai ita maganar ‘yansandan Jiha an dade ana yin ta lokaci mai tsawo, tana bukatar gyaran tsarin mulki ne domin a samu cimma burin na kafa ta, domin kuwa ai abin ya shafi Jihohi 36 na Nijeriya.

    Shugaban kungiyar ya bayyana ra’ayin sa

    Shugaban kungiyar CSSLIN,Honorabul Emomotimi Dennis Guwor ya bayyanawa LEADERSHIP a hirar da ya yi da ita ranar Lahadi ta makon da ya gabata, inda ya ce wani lamari ne wanda  ya dace ace ya zuwa halin da ake ciki, an gama shi, ba ma kamar idan aka  yi la’akari da irin halin  tabarbarewar  tsaro da Nijeriya ta ke fuskanta yanzu, tun da ‘ yan Nijeriya sun yi maraba da shi lamarin.

    Kamar dai yadda Shugaban ya ce,Tinubu  tuni ne ya kalubalanci wadanda suke da ruwa da tsaki“su fara tunanin hanya mafi dacewa da ta kamata ayi gyaran shi tsarin mulkinsaboda a samu damar sa lamarin  ‘yansandan Jiha ko, a samu dama ita kasar Nijeriya ta samu zaman lafiya wanda ya dace, ko su fara aiki a dazuzzukan mu,a samu ceto daga masu cutar da su, ya kasance tsoro ya fita daga idon mutane.”

    Ya ce kungiyar ta Shugabannin majalisun Nijeriya ba su da wata matsala su, suna goyon bayan lamarin ba tare da wata matsala ba.

    “Yawancin ‘yan Nijeriya da wasu kungiyoyi a shekaru ashirin da suka gabata sun fara maganar duk kuma daya ce da ta shafi ‘yansanda Jiha, hakan yana nuna matukara aka kafa ‘yansandan na Jiha ita ce hanya da ta fi dacewa wadda a dalilin yin haka nana iya samun ci gaba da kuma bankwana da rashin tsaron da ake fama,  kamar yadda ya ce,”.

    Guwor, wanda har ila yau shi ne Shugaban majalisar Jihar Delta, majalisar Jihar, sun bada tabbaci da ke nuna cewar ba za ta yi wasa da lamarin ba, tun da yake yanzu shi ne ya dawo da maganar .

    Zai iya tunawa majalisar dattawa sun tabbatawar ‘yan Nijeriya cewa za su yi ma lamarin na ‘yansanda  Jiha duk yadda ya dace, ba za su yi wasa da shi ba, domin abu ne muhimmi, ba za su bari abin ya shiga wani hali ba,za su dauki abin da muhimmaci saboda kuwa ai sun san lamari ne da bai son bata lokaci, da zarar an tura  ma su ‘yan majalisa nan da nan za su yi abinda ya fi dacewa da  lamarin.Ba za su  sa ido har ace an fara yin kamfe na siyasa.

    Ya yi kira da masu ruwa da tsaki da su yi duk abubuwan da suka dace da suka san za su taimakawa kokarin da suke yi,kada su sa wata  gazawa tare da su, idan kuma an kai ga kirkiro su ‘yamsanda na Jihohi kada ayi amfani da su wajen cimma burin da ya wuce na harkar tsaro, a kuma tanaji hukunci  mai tsauri da zai hana yin amfani da su ta hanyar da bata kamata ba.

    Don haka ne ma ya tuna da, da irin maganar da mai magana da yawun ‘yan majalisar dattawa , Sanata Yemi Adaramodu, ya yi “ Za mu yi duk abinda ya dace mu yi dangane da lamarin; muna bada tabbacin kafi karshen wannan shekarar, za mu yi duk gyare- gyare da suka kamata, wabda hakan ne za mu samu dama ta kirkiro’yansandan Jiha.”

    Guwor  ya ce ita maganar  tsarin ‘yansandan Jiha babu wata matsala ba ce ta kanta saboda ana iya amfani da ita domin taimakawa al’umma.

    “Maganar gaskiya matsalar ita ce Nijeriya ba kasafai ake yin abubuwa kamar yadda doka ta shinfida ba, inda kuma ba’a kiran mutane su yi bayani akan abubuwan da suka yi da basu dace ba. Hakanan a wurin da ba ‘a iya daukar mataki na hukuntawa kan wadansu abubuwan da aka ki yi hakanan,a irin wannan hali masu irin wadancan halayen za su yi dukkan abubuwan da suka dama. Hakanan ma babu wata maganar kage, ana iya yin amfani da dansanda ayi abinda aka dama ta ko wane irin hali — ko dai a karkara, Jiha ko kuma tarayya, matukar har duk wadanda suke jagorancin wuri za ‘a kyale su, su yi ta yin abubuwan da suka daman a karya doka.”

    [ad_2]

    Source link

  • Ministan Wajen Sin Ya Zanta Da Takwarorinsa Na Afghanistan Da Holland

    [ad_1]

    A jiya Juma’a, ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi, ya tattauna ta wayar tarho tare da takwarorinsa na kasashen Afghanistan da Holland.

    Yayin zantawar ministan wajen kasar Afghanistan Mawlawi Muttaqi, ya gaya ma Wang Yi cewa, kasarsa na godiya ga kasar Sin bisa kokarinta na sulhunta Afghanistan da Pakistan.

    A nasa bangare kuwa, Wang Yi ya ce, a lokacin da ake fuskantar karin rikice-rikice a duniya, ya kamata kasashe makwabta su kara hadin kai wajen tinkarar matsaloli daban daban, da nemo hanyar tabbatar da tsaronsu na bai daya.

    Wang Yi ya kara da cewa, kasar Sin tana daukar matsayi na adalci, da na rashin karkata ga wani bangare, yayin da take sulhunta Afghanistan da Pakistan, tana kuma fatan ganin bangarorin 2 sun yi kokarin samun natsuwa da yin hakuri, sa’an nan su koma teburin shawarwari, don tabbatar da damar tsagaita bude wuta cikin sauri, da daidaita sabanin ra’ayi ta hanyar tattaunawa.

    Ban da haka, ministocin 2 na Sin da Afghanistan, sun yi musayar ra’ayi kan batutuwa masu alaka da yakin da ake yi a kasar Iran, inda Wang Yi ya ce kasar Sin na son yin hadin gwiwa da gamayyar kasa da kasa, a kokarin gaggauta maido da zaman lafiya a yankin da kasar Iran ke ciki.

    Ban da haka, duk dai a jiya Juma’a, Wang Yi ya tattauna da ministan wajen kasar Holland Tom Berendson, inda jami’an biyu suka jaddada aniyar kasashensu ta karfafa hadin gwiwa tsakaninsu, kafin daga bisani suka yi musayar ra’ayi kan batun da ya shafi yakin da ake yi a kasar Ukraine. (Bello Wang)

    [ad_2]

    Source link

  • Gidauniya ta tallafa wa mutum 38 da Naira miliyan 2.35 a Gombe

    [ad_1]



    Gidauniyar Zakka da Wakafi a Jihar Gombe, ta raba Naira miliyan 2.35 ga mutane 38 marasa galihu domin tallafa musu a lokacin watan Ramadan.

    Tallafin na daga cikin ƙoƙarin da gidauniyar ke yi na taimaka wa mata da matasa su samu sana’o’i da dogaro da kai.

    Shugaban gidauniyar, Dokta Abdullahi Abubakar Lamido, ya ce an kafa gidauniyar ne domin amfani da zakkar Musulunci, sadaka da waƙafi wajen rage talauci da kuma taimaka wa marasa ƙarfi a cikin al’umma.

    Ya bayyana cewa tun a shekarar 2017 wasu masana a Jihar Gombe suka fara tattaunawa kan yadda za a tsara tsarin zakka domin taimaka wa marasa galihu.

    Daga baya aka yi wa gidauniyar rijista da Hukumar Kula da Kamfanoni (CAC) a shekarar 2019.

    Lamido, ya ce manufar gidauniyar ba kawai raba kuɗi ba ne, tana son mutane su koyi sana’a su zama masu dogaro da kansu.

    “Manufarmu ita ce mu taimaka wa mutane su tashi daga masu karɓar tallafi su zama masu bayarwa a nan gaba,” in ji shi.

    Tun bayan kafuwarta, gidauniyar ta gudanar da shirye-shirye da dama kamar tallafin karatu ga ɗalibai marasa galihu, taimakon marayu, rabon kayan abinci, da kuma horar da mata sana’o’i.

    A bana, gidauniyar ta kammala zagaye na tara na shirin tallafa wa mata domin su fara sana’o’i.

    Haka kuma ta shirya shan ruwa da marayu da marasa galihu, tare da rabon kayan abinci ga masu buƙata.

    Gidauniyar ta kuma fara wani sabon shiri na kai abincin buɗa-baki zuwa asibitoci domin taimaka wa marasa lafiya da masu kula da su.

    A wajen rabon tallafin, Madakin Gombe, Alhaji Umar Abubakar, da Injiniya Ibrahim Kawuwa, shugaban kwamitin shirya taron, sun yaba da ƙoƙarin gidauniyar.

    Sun kuma roƙi al’umma musamman masu hannu da shuni da su ci gaba da tallafawa irin waɗannan ayyukan alheri domin taimaka wa marasa galihu.


    [ad_2]

    Source link

  • Shin kun san kamfanin da ke yin galibin kayayyakin da muke amfani da su?

    [ad_1]



    Wataƙila kullum kana amfani da kayayyakin wannan kamfani ba tare da ka sani ba (#Mu Ne)

    ’Yan Najeriya suna ɗaukar kayayyakin da suka saba amfani da su da matuƙar muhimmanci. Akwai kayayyakin gida da muka fi so, abincin da muka tashi muna ci tun muna yara, da kuma wasu kayayyaki da muka dogara da su a rayuwarmu ta yau da kullum. Amma ka taɓa tsayawa ka yi tunani kan tambari ko kamfanin da ke yin waɗannan kayayyakin?

    Akwai wani babban kamfani da ke aiki a fannoni da dama a Najeriya — daga abincin da muke ci a gidajenmu, zuwa samar da kayan aikin noma, masana’antu, da kuma harkokin sufuri da rarraba kaya.

    A kullum muna mu’amala da wasu rassan kamfanoninsa daban-daban, amma babban kamfanin da ke samar da waɗadannan kayyyaki yana taka muhimmiyar rawa a tattalin arzikin ƙasar ba tare da mutane da yawa sun lura ba.

    Yanzu lokaci ya yi da za a gwada fahimtar da kuke da ita game da manyan kamfanoni a Najeriya. Kafin a bayyana amsar a cikin ’yan kwanaki masu zuwa, bari mu ga waɗanda suka fi sanin kasuwannin ƙasar.

    To ga tambaya ga masu amfani da Nairaland: Ba tare da amfani da shafin Google ba, wane kamfani ne ake magana a kai?

    Ko za ku iya cankar ko wane kamfani ne. Mu gani wa zai iya canka daidai.


    [ad_2]

    Source link

  • Tun Ina Karama Nake Sha’awar Harkar Wasan Kwaikwayo —Fartima Hamza

    [ad_1]

    Shafi ne da ya saba zakulo muku fitattun jaruman finafinan hausa manya da kanana daga cikin masana’antar shirya finafinan Hausa ta Kannywood, inda a yau shafin ya yi cozali da wata jarumar mai suna FATIMA HAMZA wacce aka fi sani da FATI GWARAMA. A yayin da take bayyana wa masu karatu yadda aka yi ta tsinci kanta a cikin masana’antar Kannywood, ta bayyana wasu halaye da wasu daga cikin ‘yan masana’antar suke da ita. Haka kuma jarumar ta yi kira ga masu kokarin shiga cikin masana’antar tare da basu shawarwari, har ma da wasu batutuwan masu yawa.

    Ga dai tattaunawar tare da wakiliyar jaridar LEADERSHIP HAUSA RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:

    Da farko za ki fadawa masu karatu cikakken sunanki

    Sunana Fatima Hamza Adam wacce aka fi sani da Fati Gwarama.

    Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

    An haife ni a garin Lagos, amma na girma a garin Kano. Mahaifiya ta haifaffiyar garin Kano ce, mahaifina mutumin Bauchi ne. Nayi karatu na tun daga firamare har zuwa sakandire a garin Kano.

    Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma harkar fim?

    Tun ina karama nake da sha’awar harkar wasan kwaikwayo, saboda har a makaranta ni ce wacce nake jagorantar ‘Hausa Club’. Sannan da na gama karatu ban bayyanawa mahaifana ba saboda mahaifina da ya fara jinyar ajali har sai da Allah yayi ikonsa. Bayan rasuwar mahaifina na shaidawa mahaifiyata, daga nan ta ba ni goyan baya.

    Kina so ki ce baki fuskanci wani kalubale daga wajen mahaifiyarki ba kenan?

    Eh, ban samu wani kalubale sosai a kanta ba, saboda irin yaddar da ta yi min.

    Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?

    To, a gaskiya na fuskanci kalubale saboda mu hausa fulani bamu fiya yadda da fim ba, amma saboda mahaifiyata ta goyamin baya sai abin ya zo min da sauki. Sai bayan ita ma Allah ya yi mata rasuwa sannan kuma kalubalan ya kasance, amma dai Alhamdulillah.

    Da su wa ki ka fara cin karo a farkon shigarki masana’antar kannywood?

    Na fara haduwa da su Lawan Ahmad, Salisu S. Fulani, Ali Rabi’u Ali Daddy, Aminu Asarab da dai sauran.

    Da wane fim ki ka fara?

    Sunan fim din ‘Cikin Wane’, wanda ‘director G Sharif’ ya bada umarni.

    Ya farkon farawar ta kasance?

    Akwai wani furodusa ana kiransa da Ali bet, shi kuma dan unguwar mu ne. A sanadiyyar sa muka hadu da ‘director’ daga nan sai ya bani ‘roll’ din jarumar fim din gabadaya.

    Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?

    Na yi finafinai sun kai kamar guda ashirin ko sama da haka.

    Ko za ki iya fadawa masu karatu sunayen kadan daga finafinan da ki ka fito ciki?

    Eh, a gaskiya suna da yawa, sai dai na fada miki wasu daka ciki; “A Wani Gida, Kakanda, Maryama, Izzar so, Hujja, Ki Yafe Ni, da dai sauransu.

    A finafinan da ki ka fito ciki wanne ne ya zamo bakandamiyyarki, kuma me ya sa?

    Duk fim din da na fito ciki ina son shi amma na fi son fim din ‘A wani Gida’, saboda na sha wahala sosai, kuma ina cikin dimuwar rashin mahaifiyata. Sannan kuma an yi tunanin ba zan iya ba, saboda halin da nake ciki, amma kuma daga karshe sai nayi abin da ba a yi tunani ba, sanadin hakan na sami alkairi sosai.

    Wane irin nasarori ki ka samu game da fim?

    Na sami nasarori sosai asanadiyyar fim wanda ba zan iya shaidawa ba amma dai Alhamdulillah an sami nasara.

    Wane irin kalubale ki ka taba fuskanta game da fim?

    Eh! to, kinsan kowace sana’a da nata kalubalen kuma ni kaina na fuskanci kalubale sosai, musamman ma a tare da abokan sana’ar mu. Saboda wasu daga cikinsu ba sa san cigaban wani wanda ya zo bayansu, sannan kuma wasu daga cikinmu suna sa kyashi, ga kuma wani lokacin ban gishiri ne na baka manda.

    Bayan klubalen da ki ka fuskanta, ko akwai wani abu da ya taba faruwa da ke na farinciki ko akasin haka wanda ba za ki taba iya mantawa da shi ba a rayuwar ki?

    Abin da ba zan iya mantawa da shi ba shi ne, rashin mahaifana da nayi a cikin shekara daya, ba zan taba iya mantawa da shi ba. Saboda ina matukar kewar mahaifana sosai.

    Wane ne ubangidanki a masana’anyar Kannywood?

    Ai Kinsan babu wani wanda yake ci gaba ba tare da agazawar wani ba, Ali Bet shi ne ubangidana na farko a cikin wannan masana’antar tamu.

    Kafin shigarki masana’antar Kannywood wadanne jarumai ne suke burge ki, kuma me ya sa?

    Eh! to, babu jaruman da nake so kamar Hafsa Shehu, da kuma Ahmad S. Nuhu ina sansu sosai. Saboda san da nake mata har bikinta sai da aka kai ni kuma na je gidanta tana amarya muka yi sabani, na takaice miki da Ahmad ya rasu a gidanmu ranar babu wanda ya karya saboda ina ta kuka, babana ya mutu to, wadannan sune wadanda nake so.

    Mene ne burinki na gaba game da fim?

    To, burina shi ne na ga muna hada kanmu muna cire hassada, sannan kuma ina san na ga na kawo sauyi a cikinta da ci gaba.

    Ya batun aure, yaushe ki ke saka ran yin aure.

    Shi ai aure lokaci ne, kuma koyaushe ya zo ina maraba da shi.

    Ko akwai wani jarumi da ya taba cewa yana sonki zai aure ki cikin masana’antar?

    Eh to, akwai wani wanda muka taba batun aure da shi amma ba zan iya bayyana shi ba.

    Bayan fim kina wata sana’ar ne?

    Eh ni marubuciya ce ta finafanai, sannan kuma ina yin kasuwanci.

    Wasu daga cikin masana’antar Kannywood na kokawa game da masana’antar, shin wace ce ita, kuma ya cikinta yake?

    To, kowace sana’a akwai daidai akwai ba daidai ba, sannan kuma masana’antar fim masana’anta ce wacce duk abin da ka zo da shi take karbarka, kuma masana’anta ce wacce za a sami duk wani abu da aka zo domin shi.

    Ko akwai wani kira da za ki yi ga masu kokarin shiga cikin masana’antar?

    Duk wani wanda yake san wannan sana’ar ya shigo da niyya mai kyau, Saboda duk abin da ka zo domin shi, shi kake samu.

    Me za ki ce da masoyanki masu kallon finafinanki?

    To masoyana na fadin duniya ina mai farinciki da kaunar ku gare ni, sannan kuma ku jira ku ga irin tanadin da nayi muku a cikin wannan shekarar. Ina gaida duk wani masoyina da ma wanda ba ya sona, duk ina yi musu fatan alkairi.

    [ad_2]

    Source link

  • Mutum 10 sun rasu yayin artabu tsakanin sojoji da ’yan bindiga a Filato

    [ad_1]



    Aƙalla sojoji uku da ’yan sa-kai bakwai ne, suka rasu yayin wani artabu da ’yan bindiga a ƙauyen Wanka da ke yankin Keram a Ƙaramar Hukumar Kanam ta Jihar Filato.

    Mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin ranar Juma’a, lokacin da ’yan bindiga suka shiga ƙauyen suna harbe-harbe.

    Rahotanni daga mazauna yankin sun nuna cewa sojoji uku da ’yan sa-kai bakwai ne sun rasa rayukansu yayin artabun.

    An kuma ce wasu daga cikin ’yan bindigar sun mutu a yayin arangamar.

    Wani mazaunin yankin, Gambo Musa, ya ce wasu kyaftin biyu daga rundunar sojojin na cikin waɗanda suka rasu.

    Ya bayyana cewa mazauna ƙauyen sun daɗe suna rayuwa cikin barazanar ’yan bindiga, inda a cewarsa ’yan bindigar kan shiga ƙauyen su aikata abin da suke so sannan su tafi.

    Musa, ya ce tun da safiyar ranar Juma’a ne jami’an tsaro ƙarƙashin jagorancin wasu kyaftin guda biyu suka shiga ƙauyen suka fafata da ’yan bindigar, inda aka kashe wasu daga cikinsu yayin da wasu suka tsere zuwa cikin daji.

    Sai dai bayan wasu sa’o’i, kafin sojojin su bar yankin, ’yan bindigar sun sake haɗuwa a cikin dajin, suka dawo suka kai wa sojoji da ’yan sa-kai da ke taimaka musu hari.

    “’Yan bindigar sun dawo daga cikin daji suka kai hari kan jami’an tsaro. An yi musayar wuta mai tsanani wanda ya janyo asarar rayuka a ɓangarorin biyu,” in ji Musa.

    Wani mazaunin yankin, Ibrahim Ubale, ya ce harin ya yi muni, inda ya bayyana cewa ’yan bindigar sun je da muggan makamai, lamarin da ya ba su damar yin fito-na-fito da sojoji da ’yan sa-kai.

    “An yi musayar wutar na wasu mintuna, amma har yanzu ba a tabbatar ko akwai wasu mazauna ƙauyen da abin ya shafa ba,” in ji shi.

    Da aka tuntuɓi kakakin rundunar Operation Enduring Peace, Kyaftin Polycap Oteh, bai amsa kira ko saƙonnin waya ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

    Rahotanni sun nuna cewa ƙauyuka da dama a ƙananan hukumomin Wase da Kanam, waɗanda ke maƙwabtaka da juna, sun daɗe suna fuskantar hare-haren ’yan bindiga.

    A watan da ya gabata, rundunar sojin Najeriya ta tura sojoji kusan 300 zuwa yankin domin taimakawa wajen yaƙi da ’yan bindiga, satar mutane da sauran ayyukan ta’addanci.


    [ad_2]

    Source link

  • Mutum 10 sun rasu yayin da sojoji suka yi artabu da ’yan bindiga a Filato

    [ad_1]



    Aƙalla sojoji uku da ’yan sa-kai bakwai ne, suka rasu yayin wani artabu da ’yan bindiga a ƙauyen Wanka da ke yankin Keram a Ƙaramar Hukumar Kanam ta Jihar Filato.

    Mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin ranar Juma’a, lokacin da ’yan bindiga suka shiga ƙauyen suna harbe-harbe.

    Rahotanni daga mazauna yankin sun nuna cewa sojoji uku da ’yan sa-kai bakwai ne sun rasa rayukansu yayin artabun.

    An kuma ce wasu daga cikin ’yan bindigar sun mutu a yayin arangamar.

    Wani mazaunin yankin, Gambo Musa, ya ce wasu kyaftin biyu daga rundunar sojojin na cikin waɗanda suka rasu.

    Ya bayyana cewa mazauna ƙauyen sun daɗe suna rayuwa cikin barazanar ’yan bindiga, inda a cewarsa ’yan bindigar kan shiga ƙauyen su aikata abin da suke so sannan su tafi.

    Musa, ya ce tun da safiyar ranar Juma’a ne jami’an tsaro ƙarƙashin jagorancin wasu kyaftin guda biyu suka shiga ƙauyen suka fafata da ’yan bindigar, inda aka kashe wasu daga cikinsu yayin da wasu suka tsere zuwa cikin daji.

    Sai dai bayan wasu sa’o’i, kafin sojojin su bar yankin, ’yan bindigar sun sake haɗuwa a cikin dajin, suka dawo suka kai wa sojoji da ’yan sa-kai da ke taimaka musu hari.

    “’Yan bindigar sun dawo daga cikin daji suka kai hari kan jami’an tsaro. An yi musayar wuta mai tsanani wanda ya janyo asarar rayuka a ɓangarorin biyu,” in ji Musa.

    Wani mazaunin yankin, Ibrahim Ubale, ya ce harin ya yi muni, inda ya bayyana cewa ’yan bindigar sun je da muggan makamai, lamarin da ya ba su damar yin fito-na-fito da sojoji da ’yan sa-kai.

    “An yi musayar wutar na wasu mintuna, amma har yanzu ba a tabbatar ko akwai wasu mazauna ƙauyen da abin ya shafa ba,” in ji shi.

    Da aka tuntuɓi kakakin rundunar Operation Enduring Peace, Kyaftin Polycap Oteh, bai amsa kira ko saƙonnin waya ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

    Rahotanni sun nuna cewa ƙauyuka da dama a ƙananan hukumomin Wase da Kanam, waɗanda ke maƙwabtaka da juna, sun daɗe suna fuskantar hare-haren ’yan bindiga.

    A watan da ya gabata, rundunar sojin Najeriya ta tura sojoji kusan 300 zuwa yankin domin taimakawa wajen yaƙi da ’yan bindiga, satar mutane da sauran ayyukan ta’addanci.


    [ad_2]

    Source link

  • Wane Irin Tanadi Kuka Yi Wa Sallah Karama A Wannan Lokacin?

    [ad_1]

    Shafin TASKIRA shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban daban da suka shafi al”umma, cikin sun hadar da; zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya da dai sauransu.

    Tsokacinmu na yau zai yi duba game da abin da ya shafi Sallah Karama. Inda shafin ya ji ta bakin wasu daga cikin ma’abota shafin game da wannan batu; “Wane irin tanadi aka yi wa Salllah Karama a wannan lokacin?, A kowacce shekara akan fitar da wasu nau’ikan kaya na sakawa wadanda ake fitar musu da sunaye daban-daban na yayi, shin ko wannan sallar an yi mata tanadin kaya na musamman?, Wacce shawara za a bawa matasa da kuma iyaye game da kayan Sallah, musamman wadanda Allah bai hore musu da kaya me yawa ba?”.

    Ga dai bayanan nasu kamar haka:

    Sunana Badariyya Muhammad, Jihar Kano:

    Gaskiya wannan sallar an yi mata tanadi da yawa, musamman kayan adon na mata aka tanada, kamar takalmin da za a yi yayinsa me suna Shafa Wali, sai kuma Hijab me sarka me suna Capacity, sai atamfa me ‘stones’. Kayan da aka tanada kenan a wannan sallah in sha Allah. Sannan ina kira ga ‘yan’uwa mata musamman matasa ‘yan’uwanmu da su rage buri, kuma su yi hakuri da iya abin da iyaye suka yi musu, kada ki ce lallai sai ke ma an yi miki Shafa Wali ko kuma Capacity, ki yi hakuri domin duk kudi gare su ba wai sauki ne da su kamar ruwan sha ba. Abin da Allah ya horewa iyayenka ka yi hakuri da shi, kar ka je kana roko wajen saurayi ko bayar da kai dan neman kudin atamfa me ‘stones’

    Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos, Jihar Filato:

    Cikin yardar Allah nan da mako mai zuwa ana shirye-shiryen kammala azumi da gudanar da bikin Sallah Karama. Tun kafin ganin watan Ramadan wasu da dama sun fara shirin tunkarar bikin sallah, musamman wadanda ke fargabar samun akasi daga wajen tela. Shi ya sa mako guda da shigar azumi har wasu teloli na cewa sun rufe karbar dinkin sallah, sai na idon kunya. Saboda yadda aka yi gaggawar kai dinkuna da wuri. Kamar yadda yake bisa al’ada kowacce shekara ba a rasa irin salon dinki ko kayan da za a ce akwai yiwuwar za a yi yayinsu a bana, musamman ga yara da mata. Manya ma suna da irin nasu kayan da ake sa ran ganin su da yawa a jikin mutane, kamar dinkin yadi da babbar riga mai aikin zare na zamani. Su kuma mata dogayen riguna na Abaya da hijabai masu salon dinki daban-daban. Nasihata ga ‘yan’uwa musulmi maza da mata shi ne, kada a tsawwala wa kai, ko a yi buri fiye da abin da Allah ya hore mana. A yi dinki na mutunci, tarbiyya da tsare al’ada. Kuma a guji matsawa har a ciwo bashi don a yi irin dinkin wance ko gyaran jiki irin na wance ba. A yi shirin sallah daidai misali. Kadaran Kadahan!

    Sunana Hassana Iyayi Yahaya (Maman Noor), daga Jihar Kano:

    Allah ya kai mu lafiya shi ne babban tanadin, Hmmm Aikuwa wannan shekarar an fitar kala-kala ma kuwa sai fatan Allah hore abin siya. Wanda Allah bai hore ba a wanke na Bara a saka shi ne lafiya lau.

    Sunana Aminu Adamu, Malam Madori, A Jihar Jigawa:

    To magana ta gaskiya al’amarin sallah a wannan shekara sai mu ce Alhamdullilah, domin hidimar sallah daidai gwargwado mun yi muna kuma kan yi har zuwa lokacin sallah. To, magana sutura ta yayi ko akwai ta ma domin ni shadda nafi amfani da ita musamman lokacin bukukuwan sallah dama bukukuwan aure ko suna, don mu shadda ce adon mu na sallah insha’Allah. To, shawarata a nan ita ce ya kamata mutum yayi amfani da irin damar da yake da ita kada yayi gasa ko koyi da wani wanda yafi karfin sa wajen gudanar da hidimar sallah, kuma mu dage da yi wa kasar mu Najeriya addu’ar samun zaman lafiya a wannan kwanaki masu albarka.

    Sunana Sadiya Abubakar Maru, daga Gombe:

    Ba a rasa nono a riga, wannan abu ne da kowa ya sani tun fil azal. Al’umma sun fara tanadin sallar bana tun da wuri ta hanyar sayen kayan sawa da kuma bada dinki da wuri domin gudun samun matsala daga wajen tela. Shekarar bana ma ta zo da sabon salo kamar yadda aka saba a kowace sallah. Kamar yadda yake yawo a kafafen sada zumunda, akwai hijaabi mai capacity, takalmin shafa wali, da zani mai ‘stone’ wanda mutane da dama ke nema ido rufe. Shawarata ita ce kowa ya daga hannu ya kalli yatsun hannunsa, zai ga ba daidai suke ba. Wannan yana nuni da cewa daidai ruwa daidai gari. Kada a takura kai wajen yin abin da karfin mutum bai kai ba, ayi mika daidai da abun rufa. Idan Allah ya hore miki ki yi, idan bai hore miki ba kada a duma kai.

    Sunana Muhammad Isah, Zareku Miga A Jihar Jigawa:

    Sallar Bana Alhamdulillahi domin ta zo cikin saukin tsadar rayuwa. Saboda kayan abinci ya zo da dan sauki. Eh a Bana mata a garin mu sun fi yin Ankon LESHI DA SHADDA SHAMPOO. Shawara da zan bawa matasa  da ma iyaye shi ne su tuna idan bana Allah bai hore miki ba to, a baya ai an yi sabbin kaya kala-kala a saka hakuri idan Allah ya so nan gaba sai a dinka sabbin kaya. A samu mai kyau a saka a tafi masallacin Idi.

    [ad_2]

    Source link

  • An Kai Hari Da Jirgin Sama Maras Matuƙi Kan Ofishin Jakadancin Amurka A Baghdad

    [ad_1]

    Wani hari da jirgin sama maras matuƙi ya afkawa ofishin jakadancin Amurka a Baghdad, lamarin da ya sake tayar da hankula a yankin Gabas ta Tsakiya yayin da rikici ke ƙara tsananta tsakanin Amurka, Israel da Iran.

    Rahotanni sun ce fashe-fashe sun girgiza wasu birane a yankin a ranar Asabar, yayin da aka kai hari karo na biyu kan ofishin jakadancin Amurka tun daga ranar 28 ga Fabrairu. An kuma ga hayaƙi mai kauri yana tashi daga tashar jiragen ruwa ta Fujairah, ɗaya daga cikin manyan wuraren adanawa da fitar da man fetur a United Arab Emirates.

    • Amurka Ta Yi Watsi Da Nadin Mojtaba Khamenei’ Sabon Shugaban Iran
    • Amurka Ce Tushen Matsalar Da Ake Ciki Dangane Da Batun Nukiliyar Iran

    Rikicin ya ƙara tsananta bayan hare-haren jiragen sama marasa matuƙa, da makamai masu linzami da hare-haren sama da aka ruwaito sun yi sanadin mutuwar sama da mutane 1,200 a Iran, a cewar ma’aikatar lafiyar ƙasar. Haka kuma an ce Iran ta kai hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙi kan aƙalla ƙasashe 10 maƙwabta, abin da ya dagula zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz.

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya tabbatar da cewa sojojin Amurka sun kai hari kan tsibirin Kharg Island, babban cibiyar fitar da man fetur ta Iran, inda aka kai hari kan wuraren soja amma ba a lalata cibiyoyin mai ba.

    Rahotanni sun kuma ce tsohon jagoran Iran, Ali Khamenei, ya mutu a farkon hare-haren da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar, yayin da aka naɗa ɗansa Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran ƙasar.

    A cewar babban Jakadan Majalisar Dinkin Duniya kan ƴan gudun hijira, rikicin ya tilasta wa kusan mutane miliyan 3.2 barin gidajensu a Iran. A halin yanzu, Pentagon ya ce sojojin Amurka da Isra’ila sun kai hare-hare fiye da 15,000 a wurare daban-daban a Iran cikin makonni biyu da suka gabata.

    [ad_2]

    Source link

  • Shawarar Abinci Ga Masu Ciwon Olsa A Ramadan

    [ad_1]

    Assalamu alaikum masu karatu, barkanmu da sake haduwa daku a wannan makon a cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Girki Adon Mata.

    A yau shafin namu zai zo muku da kalar abincin da  mai ciwon Alsa ya kamata yaci:

    Idan kina da ciwon Alsa  kina shan wahala idan kin dauki Azumi to ga shawara in sha Allah za tayi amfani.

    Daga farko dai abinci daya zuwa biyu shine zai kasance abincinki da za ki rinka ci:

    1. Na farko tuwo ya kasance kin mayar da tuwo abincinki, misali idan ansha ruwa ki samu tuwo kici sosai yadda jikinki bazaiyi nauyi ba.

    Bayan nan misalim 12am na dare ki tashi ki kara cin tuwo.

    Bayan nan sai da Asuba ki kara cin tuwo, kinga kin mayar da tuwo abincinki  a kalla kinci sau 3 ko 4.

    2.Idan Allah ya sa kina da hali, kullum ya kasance kina shan Maltina da Madara guda 2 ko 3 ma.

    Idan ansha ruwa kisha daya, idan za ki kwanta kisha daya, da Asuba kisha daya.

    Ina mai tabbatar miki da cewar in sha Allah idan kika bi wannna matakin za kuyi Azumi ba ta re da kun ta kura kanku ba.

    [ad_2]

    Source link