Babu Wani Sabani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

[ad_1]

Kyaftin din tawagar Super Eagles ta Nijeriya Wilfred Ndidi ya yi watsi da maganar rashin jituwa tsakanin Bictor Osimhen da Ademola Lookman, yana mai bayyana rashin jituwarsu a filin wasa a daren Litinin, inda Nijeriya ta doke Mozambikue a matsayin karamar rigima tsakanin manyan ‘yan wasan biyu.

Ndidi ya yi magana kan batun yayin da yake magana da ESPN bayan nasarar 4-0 da Nijeriya ta samu akan Mozambikue a gasar AFCON 2025, yana mai bayyana cewa ba wani abu bane mai matsala kawai dai ‘yan wasan ne ke neman karin fahimtar juna a yayin taka leda a cikin fili, dan wasan tsakiyar ya kara da cewa an warware lamarin cikin sauri a cikin tawagar yana mai cewa babu wani tashin hankali da ke tsakanin ‘yan wasan a halin yanzu.

“Komai yana lafiya, kuma mun shawo kan lamarin a cikin dakin sanya kaya, yanzu komai yana tafiya yadda ya kamata, hakazalika Lookman ya yi watsi da lamarin, yana sake tabbatar da girmamawarsa ga Osimhen da kuma karfin hadin gwiwa da girmama juna dake cikin tawagar, ban ga Osimhen ba, shi ne mutum na farko a tawagarmu, kowa ya san wannan shi babban dan wasan gaba ne, don haka komai ya daidaita” in ji gwarzon dan kwallon kafar Afirika na shekarar 2024.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *