Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin

[ad_1]

Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Fu Cong, ya ce Sin ta damu matuka da yadda ake neman jefa yankin gabas ta tsakiya cikin mummunan rami. Fu Cong, wanda ya bayyana hakan a jiya Laraba yayin zaman kwamitin tsaron MDD dangane da batun kasar Syria, ya jaddada cewa bai dace a yi watsi da yiwuwar fadadar kalubalen da ake ciki a Syria zuwa sauran sassan yankin ba.

Jami’in ya kara da cewa, wanzuwar tashin hankali a gabas ta tsakiya ba kawai zai ci gaba da illata rayuwar al’ummun yankin ba ne, har ma zai haifar da mummunan tasiri ga tattalin arzikin shiyyar da ma duniya baki daya.

Daga nan sai Fu ya yi kira da a gaggauta dakatar da bude wuta, da kuma aiwatar da matakan dakile bazuwar yakin, tare da hanzarta komawa teburin tattaunawa da shawarwari. Ya ce kasar Sin a shirye take da ta ci gaba da taka rawar gani, wajen lalubo hanyoyin wanzar da zaman lafiya mai ma’ana a yankin. (Saminu Alhassan)

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *