Gwamna Zulum Ya Sha Alwashin Kakkaɓe Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanai

[ad_1]

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya bayyana cewa mutane ko kungiyoyin da ke ba ‘yan ta’adda mafaka, ko nuna goyon baya, ko kuma ba su bayanai, makiyan jihar ne kuma abokan gaba ne. Ya ce, ƙarshensu ya zo, za a fara farautar su domin su fuskanci cikakken hukuncin doka.

Gwamnan ya yi wannan bayani ne a ranar Alhamis yayin wani jawabi ga daukacin al’ummar jihar a Maiduguri, inda ya ce ayyukan makiya, zagon kasa ne ga zaman lafiyar da jihar ta samu, kuma ba za a lamunta da ayyukansu ba.

Zulum ya yi Allah-wadai da sake ta’azzarar matsalar tsaro a wasu sassan jihar, yana mai cewa lamarin “yana da matuƙar tayar da hankali.”

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *