[ad_1]
Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa an raba sama da Naira Biliyan 98 a bara don ƙarfafa cibiyar kiwon lafiya ta farko a faɗin Nijeriya, wanda hakan ya zama ɗaya daga cikin manyan kudaden da aka zuba a cikin shekara guda a bangaren.
Da yake jawabi a taron lafiya na ƙasa na jam’iyyar APC zagaye na 1.0 a Abuja ranar Laraba, Shugaban ya ce an fitar da kuɗaɗen ta hanyar Asusun Kula da Lafiya na matakin farko (BHCPF) don tallafawa kuɗaɗen aiki a cikin cibiyoyin kiwon lafiya na farko sama da 8,300 (PHCs) a duk faɗin ƙasar.
- Gwamnatin Tarayya Ta Ce Ba Ta Taɓa Goyon Bayan Musguna Wa Kiristoci Ba
- Kotu Ta Sanya Ranar 23 Ga Afrilu Don Sauraron Shari’ar El-Rufai Kan Zargin Kutse A Wayar Ribadu
Shugaban wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume ya wakilta, ya ce rarraba kuɗin wani ɓangare ne na babban ƙoƙarin gwamnati na sake fasalin ɓangaren kiwon lafiya a matsayin ginshiƙin ci gaban ƙasa.
A cewar wata sanarwa da kakakin sakataren gwamnatin tarayya, Yomi Odunuga ya fitar, Tinubu ya bayyana cewa tallafin kudi ya taimaka wajen ci gaba da farfado da cibiyoyin kiwon lafiya na gaggawa (PHCs), inda aka riga aka inganta cibiyoyi 2,565, yayin da wasu 1,456 ke fuskantar gyaran hali a yanzu.
[ad_2]
Source link