An kama mutum 2 kan zargin shigar da ƙwaya a gidan yari

[ad_1]



Jami’an Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Najeriya reshen jihar Kano, ta ce ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da yunkurin safarar miyagun kwayoyi da kuma tabar wiwi a gidan yarin jihar.

Waɗanda ake zargin sun haɗa da: Usman Khalid mai shekara 25 da Bello Musa Ahmed mai shekara 24 dukkan su maza ne kuma mazauna unguwar Tsamiya (a Breget) a cikin jihar Kano.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gidajen yarin jihar, CSC Musbahu Lawal Kofar-Nassarawa ya fitar, ya ce an kama mutanen ne a lokacin da suke ƙoƙarin shigar da miyagun ƙwayoyin zuwa cikin gidan yarin.

Ya ce, jami’an da ke cibiyar Hukumar a yankin Goron Dutse, Kano ne suka kama waɗanda ake zargin, a lokacin da suke ƙoƙarin shigar da tabar wiwi ga fursunonin a harabar gidan,” in ji shi.

Hukumar ta gargaɗi mutane kan yunkurin shiga cikin fursunoni, musamman lokacin zirga-zirga zuwa kotu, saboda irin barazanar tsaro da hakan ke tattare da shi, kuma yin hakan akwai hukunci mai tsauri.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *