Lokaci Ya Yi Na Kawo Karshen Kashe-kashen Da Ake Yi A Kano
[ad_1]
Shugaban kungiyar masu sayar da ganyaye da kayan marmari a Kasuwar Utako Babban Birnin Tarayya Hamza Mu’azu Karwai ya yiu kira da ‘yan malisar Jihar Kano da cewar lokaci ya yi da za suyi doka wadda zata yi maganin yawan kashe- kashen jama’a wadanda ba suji basu gani ba. Ko ace sun aikata wani laifi ba hakan kawai idan wani ya bushi iska sai kawai ya kashe domin ya san ko dai ma an kai shi wajen ‘yansanda har zuwa kotu daga karshe haka suke tsammami haka ne abin zai tafi kamar yadda tsaki yake yi a cikin ruwa.
Hamza ya bayyana haka ne lokacin da ya gana da manema labarai a ofinshin sa da yake cikin kasuwar, ya ce bayan yawan kashep kashen da ake yi akwai masu aikata laifi wanda suma hukuncin kashewar ya kamata ayi haka wajen kashe su kamar yadda suma suka kashe, amma ba za ayi ba. Ya kara jaddada ‘da abin ya isa ofishin gwamna sai ya kasance tamkar ma an aiki Bawa garinsu, wanda kamar yadda ya ce shi yasa wasu suke aikata haka domin sun ku san gajiya da jin labarin irin laifukan da ake aikatawa masu nasaba da kisan kai.
- Jakadan Sin: Cudanyar Al’adu Za Ta Taimaki Yunkurin Daidaita Hulda Tsakanin Sin Da Amurka
- Fasahar Electronic Call-up Da NPA Ta Wanzar Ta Samar Da Sauki —Tsohon Kwaminsihan Sufuri
Ya ce kamar yadda ya sani ‘ Ai dama su ‘yan majalisa aikinsu shi ne yin doka to don Allah da Annabi ina kira gare ku da ku gaggauta kirkirar kudurin dokar, bayan duk an yi abubuwan da suka kamata, daga nan sai a kai ma Gwamna domin sa hannunsa
Ya bada misalai na wadanda suka rasa rayukansu kamar haka an kashe Fatima Abubakar da ‘ya’yanta shida 2026 a unguwar Dorayi Chiranchi, Kano.
‘Yan sanda sun kama mutum uku da ake zargi, tare da gano makamai da tufafi masu jini a hannunsu.
Kisan Nafiu Hafiz (2023 – Unguwa Uku, Kano)
Wata matar aure mai suna Hafsat ana zargin ta da kashe Nafiu Hafiz, wanda ya kasance ɗan gidan da suke zaune. Akwai kuma kashe Hanifa da aka yi a shekarar 2021 shi ma d Kano.
Yarinya ‘yar shekara biyar, Hanifa, malamin ta Abdulmalik Tanko ya sace ta, daga bisani ya kashe ta. Kotu ta yanke masa hukuncin kashewa.
Kisan Ummita da Dan China ya yi shekarar 2022 a Janbulo, Kano, wani dan kasar China har ila yau, Geng Kuangron, ya kashe budurwarsa Ummulkulsum Sani Buhari (Ummita) ta hanyar soka mata wuka.Shi ma ya amsa cewa shi ne ya aikata laifin a kotu. Sai kuma Mahaifiyar da ta kashe ‘ya’yanta biyu 2020 cikin unguwar Sagagi, Kano)
Sai kuma wata uwa da ta kashe ‘ya’yanta biyu, Yusuf Ibrahim mai shekara (5) da kuma Zahra’u Ibrahim da ke da shekara (3).
An ce ta aikata hakan ne sakamakon matsalar tabin hankali bayan barazanar kishiya daga miji.
Ya yi kira da ‘yan majalisar mataki za su dauka na gaggawa domin idan sun yi dokar Gwamna ya sa hannu, ba sa hannun ake so kadai ba, akwai maganar aiwatar da doka, shi ma gwamnan yana tunatar da shi ba ajiiyewa zai yi ba, hannu ya dace ya sa domina gabatar da umarni na ratayew ko kashewa,
[ad_2]
Source link