Yadda Shigo Da Shinkafa Daga Kasashen Waje Ya Share Masana’antu 90 A Nijeriya


Bangaren shinkafar Nijeriya, wanda ya jawo jari mai yawa na cikin gida da na waje, yana fuskantar gagarumin rugujewa saboda kara shigo da shinkafa da ayyukan fasa-kauri da rashin daidaiton farashi.

Darakta janar na kungiyar masu sarrafa shinkafa ta Nijeriya, Dakta Andy Ekwelem, ya ce, “Daga cikin masana’antun shinkafa sama da 150 a fadin kasar nan, kusan 90 sun dakatar da ayyukansu. Masana’antun da suka rage a halin yanzu suna aiki tsakanin kashi 30 zuwa 70 na karfin da ya rage musu.”

  • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya 
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

Rahotanni sun bayyana cewa manyan kalubalen da manoma da masu sarrafa kayan noma ke fuskanta, sun hada da yawan shigo da shinkafa da kuma fasa-kaurin kayan zuwa cikin kasar wanda ya haifar da rugujewar farashi.

Kididdiga daga wasu hanyoyi daban-daban sun nuna cewa Nijeriya ta shigo da shinkafa tsakanin tan miliyan 2.4 da 3.2 a shekarar 2025, mafi yawanci a lokacin rangwamen haraji na wucin gadi da aka yi don rage farashin abinci.

“An kiyasta shigowar shinkafa kasuwa a tsakanin shekarar 2024 zuwa 2025, tan miliyan 2.4, an samu karuwar kashi 60 cikin dari idan aka kwatanta da kiyasin watan Afrilu 2024 na tan miliyan 1.5. Wannan ba ya hada da yawan shinkafar da aka shigo da ita ba bisa ka’ida ba a cikin kasa,” a cewar bayanai daga Bestance, kamfani mai ba da shawara a fannin aikin gona.

Duk da raguwar samar da shinkafar gida, shigowar shinkafar wanda aka kiyasta ta kusan naira tiriliyan 1, sun haifar da yawan kaya fiye da bukata tun shekarar da ta gabata, wanda ya sanya Hukumar Tsara Manufofin Kasuwancin Noma ta Kasa (NAPM) ta yi kira ga gwamnati da ta dakatar da shigowa da shinkafa don ceton manoma na cikin gida.

Daraktan gudanarwa na kamfanin ‘Infinera Agribusiness Ltd’, Kolawale Oye a shafinsa na LinkedIn, ya ce ko a cikin bayanan ma’aikatar abinci ta kasa, Nijeriya ta samu karin shinkafa kusan tan miliyan 1.1 zuwa Disamba 2025. Amma wannan karin ba nasara ce ta gonaki da injinan gida ba, an samu shi ne ta hanyar shigowa da kaya.”

Banciken shekara ta 2025 daga Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ya nuna karuwar kudin shigo da abinci a Nijeriya, wanda ya tashi daga naira tiriliyan 3.83 a shekarar 2023 lokacin da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya karbi mulki zuwa naira tiriliyan 7.65 a shekarar 2025.

Yawancin manoma da suka yi magana kan lamarin, sun ambaci sassaucin gwamnatin tarayya kan harajin shigo da shinkafa da wasu kayayyaki (Yuli 2024 zuwa Disamba 2025) a matsayin babban abu da ya janyo yawan shigo da kaya sosai.

Duk da haka, yayin taron hadin gwiwa na masu ruwa da tsaki a Abuja, ministan noma da samar da abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya ce an shigo da tan 250,000 kawai a wannan lokacin. Ya ce wannan adadin ba shi da girma ga bukatar cikin gida ta kasar, wanda ke kaiwa kusan tan miliyan 11.

Amma yayin da yake magana a wani taro ranar Litinin da ta gabata tare da kungiyar masu sarrafa shinkafa ta Nijeriya (RIPAN) a Abuja, karamin ministan masana’antu, Sanata John Owan Enoh, ya yarda cewa akwai matsala.

“Lokacin da aka sayar da shinkafa da aka shigo da ita ko aka safarar ta ba bisa ka’ida ba a farashin da ya yi kasa sosai da na shinkafa da ake sarrafa a gida, hakan yana rage ingancin samar da kayayyakin ciki da kuma hana jari a wannan fanni.

“Gwamnati ba za ta yi ja da baya ba wajen daukar matakan manufofi da suka dace don kare masana’antar cikin gida da kuma ci gaba da sarkar shinkafar Nijeriya,” in ji shi.

Sanata Enoh ya amince cewa karuwar yawan shinkafar kasashen waje mai arha da ke shiga kasuwar Nijeriya na haifar da barazana mai tsanani ga masana’antu na cikin gida da kuma nasarorin da gwamnatocin baya suka cimma.

Shigo da shinkafa ta kan iyakokin kasa an haramta shi a lokacin mulkin tsohon shugaba kasa, Muhammadu Buhari, wani ci gaba da ya kara yawan samar da shinkafar gida wanda ya sa kamfanonin sarrafawa su kashe miliyoyin daloli a baya.

Saboda wannan manufofi, samar da shinkafar ya tashi daga tan miliyan 2.8 a shekarar 2010 zuwa tan miliyan 8 a shekarar 2021, wadda ta kasance shekarar da aka samu shinkafa mai yawa, wanda shirin ‘Anchor Borrowers’ ya jagoranta, tare da fitar da shinkafar da aka nika tan miliyan 5.3 a kowace shekara.

Rahotanni sun bayyana cewa sakamakon ya haifar da raguwar gibin bukata wanda ya samar da shakku tare da samun karuwar tan 1.5 zuwa tan 3.5 a kowace hektar.

Yawancin jihohi, wadanda suka samu shinkafa mai yawa, sun hada da Kebbi (tan miliyan 3.5), Jigawa (tan miliyan 2.1), Kano (tan miliyan 1.6), da Ebonyi (tan miliyan 1.5) bisa ga bayanai daga Babban Bankin Nijeriya a shekarar 2022.

Tun daga shekarar 2017, an gina kimanin masana’antun noman shinkafa na matsakaici da manya guda 68 a fadin kasar, musamman a arewaci, tare da dubunnan masana’antun kanana da ke Kano, Kebbi, Kaduna, Katsina, Jigawa, Taraba, Benuwai, Nasarawa, Anambra, Ebonyi, da wasu wurare a sauran jihohi.

Amma sanata Owan Enoh ya ce, “An tattauna da yawa daga cikin wadannan batutuwan sau da dama a cikin shekaru. Manufar wannan gwamnati ba magana ba ce, amma aiwatarwa ta gaskiya wanda ke kawo sakamako ga ‘yan Nijeriya.”

Ministan ya jaddada cewa shinkafa ta ci gaba da kasancewa daya daga cikin manyan abincin yau da kullum na Nijeriya kuma tana da muhimmancin ga zaman lafiya kasar.

Ana kiyasin cewa shinkafa a Nijeriya a kilo 32–33 ga kowane mutum a shekara, wanda ya kai tan miliyan 6.7 zuwa 7 na shinkafa mai tsabta a shekara.

“Wani karfi a fannin shinkafa yana da muhimmanci ga samar da abinci, samar da aikin yi da kuma habaka ci gaban tattalin arziki,” in ji ministan.

Shugaban RIPAN, Dakta Andy Ekwelem, ya ce shinkafar da ke shigowa Nijeriya ba bisa ka’ida ba ta hanyar iyakokin kasar sabada kaurace wa haraji da kudaden shigar hukuma, wanda ke sa tana arha fiye da shinkafar da aka sarrafa a ciki gida, kuma yana sanya masu samar da shinkafa na cikin gida cikin rashin daidaito mai tsanani.

“Shinkafar da aka yi fasa-kauri tana shiga kasuwar Nijeriya a farashin da masu sarrafata a gida ba za su iya gogayya da su ba,” in ji Dakta Ekwelem. “Wannan gasa mara adalci ta yi mummunan tasiri ga masana’antar shinkafa a Nijeriya.”

Ya ce wahalar da masu sarrafa shinkafa a fadin kasar ta kasance mai tsanani.

Alhaji Usman Garba Badawa, wani mai masana’anta matsakaicin girma a Kano, ya shaida cewa kasuwancin sarrafa shinkafa yana kan samun matsala sosai saboda alamomi sun nuna cewa ba za su iya yin gogayya da kasuwa ba, saboda shinkafa ta waje ana sayar da ita da arha ko kuma daidai da farashin shinkafar gida amma za ta kasance zabi na farko ga masu saye ko da yaushe.

Ya bayyana cewa, a halin yanzu, shinkafa daga kasashen waje yawanci tana samun damar shiga kasuwar Kano cikin sauki daga kan iyakar Babura a Jihar Jigawa da sauran iyakoki daga Jihar Katsina.

“Ci gaban da shigowar shinkafar kasashen waje hakika alamar illa ce a gare mu, manufofin rufe iyakokin da gwamnatin tarayya ta sanya sun haifar da kafa masana’antu sama da 200 na shinkafa a Jihar Kano kadai, kuma an kirkiri dubban ayyukan yi a bangaren shinkafa. Duk da haka, da abin da muke gani a yanzu, akwai barazanar da ka iya tilasta rufe wadannan masana’antu gaba daya kuma ya sanya duk wadannan mutanen su rasa ayyukansu. Yanzu, a wannan lokaci mai muhimmanci na tattalin arziki, wannan lamari zai iya cutar da jama’ar Nijeriya,” in ji shi.

Dakta Ekwelem ya kara bayyana cewa manoma da masu sarrafa kayan gona suna fuskantar hauhawar farashin samar da kayayyaki, kalubalen tsaro da rashin isasshen ababen more rayuwa.

“Yawancin manoma ana tilasta musu sayar da amfanin gonarsu a asara saboda matsin lamba da shigawa da shinkafa ta haramtacciyar hanya mai rahusa. Wannan yanayi yana sanya aikin masu sarrafa shinkafa a cikin kasar ya zama mai wuya sosai a ci gaba da kasancewa mai dorewa.”

Ya kuma ce raguwar farashin shinkafa da aka gani kwanan nan a wasu kasuwanni bai kamata a dauka kamar karin samar da shinkafa a cikin gida ba, wani abu da ministan noma, Sanata Kyari, bai yarda da shi ba, yana jayayya cewa karin samarwa a cikin gida ne saboda faduwar farashi.

“Raguwar farashin ta kasance sakamakon ayyukan kungiyoyin masu fasa-kaurin kayayyaki da suke shigo da shinkafa ta hanyoyi na haram a iyakokin Nijeriya,” in ji shi.

A Kano, wakilinmu ya ba da rahoto cewa yawancin masana’antar shinkafa sun dakatar da samarwa ko suna aiki da rabin karfinsu.

Wani majiya a daya daga cikin manyan masana’antar shinkafa ta ce sun dakatar da aiki kusan watanni uku, ta kara da cewa wasu manyan masana’antar shinkafa da dama a jihar sun dakatar da samarwa, yayin da wasu kadan ke gudanar da ayyuka kadan don watan Ramadan.

A Jihar Benuwai, masu sarrafa shinkafa da yawa sun rufe ayyukansu tun bara, bayan faduwar farashi, in ji wani rahoto.

Wani dan kasuwa, Ichor Michael Tersoo, wanda ke gudanar da masana’antar shinkafa ta Wadata a Makurdi, ya shaida wa wakilinmu a Makurdi a ranar Alhamis cewa ya dakatar da kasuwancinsa saboda yana fuskantar asara.

“Na rufe kasuwancina saboda wadannan kalubalen. Ban iya kimanta kudin da na yi asara ba, ko da yake farashin shinkafar gandun daji ya fara tashi bayan durkushewa a bara.

“Yanzu ana sayar da shinkafa a tsakanin naira 50,000 da naira 55,000 idan aka kwatanta da naira 35,000 da naira 40,000 da aka saba sayarwa a shekarun ba. Amma har yanzu ban shirya yin sabon alkawari ba. Bugu da kari, hasashen wannan shekarar ya nuna cewa za a fara ruwan sama da wuri sannan kuma zai tsaya da wuri, wanda haka zai shafi noman shinkafa,” in ji shi.

Adayi Joseph Unogwu, wanda ke da sarrafa shinkafa a Wurukum cikin birnin Makurdi, ya yi kuka kan faduwar farashin shinkafa, yana cewa ba zai iya amfani da cikakken karfinsa na sarrafa shinkafa. Duk da haka, Unogwu ya rufe masana’antarsa ta Makurdi.

Ya yi kukan cewa, “Masu sarrafa shinkafa a Jihar Benuwai yana daidai da na fadin kasar. Yawancinmu ba ma aiki kamar yadda muke so, muna sarrafa shinkafa kasa da ikonmu, saboda farashin shinkafa na sauka. Wasu ma ba sa iya yin aiki gaba daya. Me ya sa? Saboda shigo da kaya ya rushe farashin shinkafar da aka sarrafa a gida.

“Babu wasu abubuwan karfafawa gwiwa kan farashin shinkafa a yanzu, wanda hakan ba shi da dorewa. Saboda shigowa da shinkafa, hakan ya sa farashin shinkafa ya kasance kasa da abin da masu iya sarrafawa da masu sayarwa ke caji. Yanzu muna da masana’antar sarrafa shinkafa da yawa wadanda ba sa aiki. Gaskiya, wasu mutane suna sayar da masana’antar shinkafarsu yayin da wasu ke ci gaba da sarrafa amma ba yadda suka so ba.

“An yi watsi da gonaki da dama, kuma manoma sun rage yawan amfaninsu saboda tsadar kayan aikin gona da kuma karancin farashin shinkafa. Don haka abin da za mu gani a cikin watanni masu zuwa shi ne rufewar masana’antu ko sarrafa kayan gona kasa da karfi da suke da shi.”

Kazalika, Gwamna Hyacinth Alia, ya bayyana shirin farfado da wannan bangare.

“A yau (Talata), na duba kayan aiki da aka samo domin farfado da masana’antun shinkafa na Jihar Benuwai a Wadata, Makurdi, wani wuri da aka yi watsi da shi tsawon shekaru amma yanzu an shirya zai ci gaba da sarrafa shinkafa.

“Wannan shiri zai kirkiri damammaki ga mata, ya karfafa kananan kasuwanci, kuma ya habaka samar da shinkafa na cikin gida a Benuwai,” in ji gwamnan a shafinsa na Facebook.

Rahotanni sun bayyana cewa dukkan manyan kamfanoni a Jihar Taraba sun rufe ayyukansu sai wasu ‘yan kanana kamfanonin sarrafa shinkafa.

An ruwaito cewa a garin Jalingo, kamfanin sarrafa shinkafa na Gamzaki da ke yankin CBN a Jalingo, da kamfanin sarrafa shinkafa na Nabinu da ke Mile 6 da kamfanin sarrafa shinkafa na Rahama da Aminci da ke Yamusala da yankin Primary Board, duk a Jalingo, babban birnin Jihar Taraba, an rufe su saboda rashin masu saye.

Mamallakin kamfanin sarrafa shinkafa na Gamzaki a Jalingo, Alhaji Aliyu Sarkin Noma, ya ce ya rufe kamfaninsa Gamzaki a Jalingo ne saboda rashin kwastomomi.

Ya ce bayan an dage haramcin shigo da shinkafa ta kasashen waje, kamfanonin sarrafa shinkafa na cikin gida sun fara rasa abokan ciniki.

Ya ce tsadar farashin dizal da na wutar lantarki da tsadar kaya sun sa kamfanoni sarrafa shinkafa rashi samun riba. Ya kara da cewa ya fara rage yawan ma’aikata a kamfaninsa kuma a karshe dole ya rufe kamfanin lokacin da babu kasuwa ga shinkafar da ake sarrafawa a gida.

Sai dai masu sarrafa shinkafan sun bayyana cewa sake bude iyakokin Nijeriya ya kara ruruta wutar lamari.

“Mutanen da ba sa noma sun yi imanin cewa bude iyakoki yana taimaka mana, amma yana cutar da samar da kayayyakin da ake sarrafawa gida fiye da amfaninsa. Shinkafa ta gida tana da karin sinadarai da dandano fiye da shinkafar da aka shigo da ita, amma da zarar shinkafar kasashen waje ta shiga kasuwa, sai a rage amfani da namu ta gida,” wani mai sarrafa shinkafa ya shaida hakan.

Masu sarrafa shinkafa sun ce masana’antun shinkafa ba za su iya tsayuwa da kafarsu ba idan har gwamnati ba ta dauki matakan da ya dace ba. Yayin da manoma ke neman samun kayan aiki a araha, masu sarrafa shinkafa suna neman manufofi da za su kare samar da shinkafar gida.

A cewar Yazid Adamu, “Mafi kyawun abin da gwamnati ya kamata ta yi shi ne, ta rage farashin kayan aikin gona. Idan aikin gona yana bukatar babban jari kuma farashin yana ci gaba da faduwa a kasuwa, mutane za su guji noma. Kuma bari in gaya muku, abin da gwamnati ba ta sani ba shi ne, lokaci zai zo da ake bukatar shinkafa ta yi yawa amma kuma samuwarta zai yi kasa sosai saboda babu wanda ke yin noma don asara.”

A dukkan fadin kasar, rahotanni sun bayyana cewa manoma da yawa ba su zuba jari a noman rani a wannan kakar ba saboda farashin kayayyakin aiki sun tashi kuma farashin shinkafar ya yi kara.

A Jihar Kano, manoman shinkafa sun ce tsadar kayan aikin gona da karancin tallafi daga hannun hukumomi, noma shinkafa ya zama abin gudu, saboda haka ma manoma da dama daga cikinsu suna tunanin barin aikin.

Daya daga cikin manoman shinkafa, Alhaji Abba Ibraheem Kallah, ya ce ya yi asara mai yawa a lokacin damina ta bana bayan ya kashe makudan kudde wajen noman shinkafa. Ya kara da cewa tsadar kayan aikin noma da kuma faduwar farashin shinkafar gida a kasuwa sun sanya da dama daga cikinsu bashi ya masu katutu. Ya ce wannan shi ne dalilin da ya sa da yawa daga cikin manoma ba su damuwa da yi noman rani.

Shugaban jiha na kungiyar manoman shinkafa ta Nijeriya (RIFAN), Alhaji Abubakar Haruna Aliyu, ya bayyana cewa fiye da kashi 50 na manoman shinkafa suna barin wannan fanni.

A cewarsa, tun bayan dakatar da shirin bai wa manoma rance a jihar, manoman shinkafa sun kasance suna daukar nauyin kansu. Ya bayyana wannan lamari a matsayin abin damuwa sosai, idan aka yi la’akari da rawar da manoman shinkafa na asali suka taka wajen tallafa wa kasar a tsawon shekaru.

“Muna da kwarin gwiwa cewa da dan taimako kadan, ‘yan kungiyarmu suna son bayar da gudunmawa ga masar da abinci a kasar nan, amma yadda abubuwa ke tafiya yanzu, na tabbata ba za mu iya shawo kansu su yi abin da ya dace ba. Duk matakan taimako sun tsaya. Manoma suna son yin haka, amma tsarin ba ya goyan bayan hakan. Dukkan batun ya canza zuwa wani abu daban. Iyakokin kasar nan da aka bude su sannan kuma aka ta shigo da shinka, yayin da samar da shinkafar gida yake mutuwa a hankali,” in ji shi.

A Nasarawa, manoman da suka karbi rance suna jin radadin asar da suka tafka wajen kokarin biyan bashin da kudin da suka samu daga sauran amfanin gona.

Manoma wadanda suka saba yin aikin gona a lokacin rani a gefen koguna da kowace fili da ake da ita kusa da ruwa sun bar noma irin wadannan gonaki.

Wakilinmu a Kano shi ma ya ruwaito irin wannan yanayi a tsibirin ban ruwa na Kadawa a karamar hukumar Kura, wani wuri da yake cike da ayyukan ban ruwa.

Wani kwararren masanin tattalin arzikin noma, Mamun Malam, ya dora laifin rikicin kan rashin tsari mai dorewa na manufofin noma na gwamnatin tarayya.

Ya ce wadata kasa da abinci zai sami tasiri sosai daga shigo da abinci.

A cewar hasashen Malam, samar da shinkafar paddy a Nijeriya zai ragu daga tan miliyan 10 a shekarar 2018 zuwa tan miliyan 4 a shekarar 2026. Ya ce saboda ambaliyar ruwa, rashin tsaro, da rashin kwarin gwiwa ga manoma, zai ragu ma fiye da haka.

Ya kara da cewa tasirin zai kara shafar sarrafawa kuma zai kara matsa lamba kan naira, saboda shigo da kaya ba kyauta ba ne.

“Masana’antar sarrafa shinkafar na rufe ayyukansu saboda wani lamari na daban da kuma rashin aiwatar da matakan noma da manufofinmu. Amma ba zai tsaya kawai ga rufe masana’antar sarrafa shinkafa ba kadai, har ma da samar da shinkafar hatsi zai ragu a wannan shekara, ba tare da daukar matakai da manufofin mulkin Tinubu ba.

“Kamar yadda gwamnati ta aiwatar na cire tallafin man fetur ba tare da shiri ba, haka ma gwamnati ya kamata ta shiga harkar shigowa da abinci ba tare da la’akari da illolinsa ba. Kuma babban illa na ba ‘yan kasuwa izinin shigowa da abinci shi ne, rage kwarin gwiwar samarwa a gida. Kunka karafaf bai wa manoma na kasashen waje kwarin giwa wadanda gwamnatocinsu suka riga suka tallafa musu ta hanyoyi da dama.

“Alhali abin da manomanmu ke bukata ko abin da tattalin arzikinmu ke bukata a kan irin wannan tallafi su ne, matakanmu na kare kanmu don dakile tallafin da masu samarwa na kasashen waje ke samu a cikin kasuwancin duniya wanda ya kamata ya zama kasuwanci kyauta. Yanzu masu samarwarmu ba su samu hakan ba, a maimakon haka ana matsa su fita daga kasuwanci.

“Idan aka duba a cikin shekarun mulkin Buhari, tsawon shekaru uku, daga 2016 zuwa 2018, Nijeriya tana samar da fiye da tan miliyan 10 na shinkafa a kowace shekara, wanda ya ragu zuwa tan miliyan 8 a kowace shekara daga 2019 zuwa 2022 saboda rashin tsaro da ambaliyar ruwa. Samar da shinkafa ya ragu zuwa kimanin tan miliyan 4 a shekarar 2025 kuma zai iya raguwa fiye da haka a shekarar 2026, kawai saboda babu abubuwan karfafa samarwa. Kuma wannan zai kara shafar sarrafa abinci kuma zai kara matsa lamba kan faduwar darajar naira.

“Babu ma’ana cewa gwamnati ta cire hannunta wajen tallafa wa bangaren samar da shinkafa, sannan ta juya ta ce bangaren ya rike kansa. Wannan lamari yana kara durkushe harkokin kasuwancin shinkafa.

“A yanzu akwai wani tsari da ake kira habaka shinkafa a kasa 2020-2030. Tsari ne mai kyau, amma sai dai idan kun ba da karin kudi ga hanyoyin samar da shinkafa ta hanyar farashi mai kyau, wato, manoma ko masu samarwa suna samun farashi mai kyau bisa kokarinsu, ba za a samu wani abin da zai fito daga wannan tsari ba. Dole ne ku ba da karin kwarin gwiwa wajen samarwa, saboda sabanin ra’ayoyi da yawa da aka yi tsammani na dogon lokaci da noman gida duk hanyoyin tattalin arziki ne wadanda kuma ke yanke shawara ta hankali da ta hada da samun riba mafi yawa,” in ji shi.

Wani rahoto a kwanan nan daga Hukumar Tsara Manufofin Kasuwancin Noma ta Kasa (NAPM) da wani kwamitin shawarwari ga shugaban kasa, sun nemi daukar mataki cikin gaggawa kan wannan al’amari.

Rahoton ya bayyana cewa kimanin manoman shinkafa 3,500 suna barin noma ko rage yawan shinkafar da suke nomawa saboda asara mai yawa, da aka kiyasta na naira biliyan 93, da aka yi a lokacin noman rani na 2025.

Binciken ya nuna cewa manoma 33,507 a jihohi 13 na gwaji kuma ya gano cewa kashi 10.6 cikin dari na manoman shinkafa suna da niyyar rage yawan amfanin gona a lokacin noman rani na shekarar 2025/2026.

A cikin rahoton kwamitin da ke bai wa shugaban kasa rawara ya kuma bayyana cewa samar da shinkafa ya ragu da kashi 7.9 a cikin lokacin damina na bara, yayin da manoma suka koma ga noman amfanin gona na kudi irin su wake, citta da alkama, wanda a yanzu ke bayar da ribar mai yawa da kuma kashe kudi kadan.

Yawancin manoman shinkafa da wakilanmu suka gana da su sun tabbatar da cewa sun kamala girbin shinkafarsu.

Daya daga cikinsu, Alhaji Shehu Garun Malam, wanda ke ikirarin cewa ya shafe shekaru yana yin noman shinkafa, ya ce zai daina noman shinkafa gaba daya.

“Sakamakon da muka samu kan shinkafa a kakar damina ta baya bai yi dadi ba kwata-kwata, har ma farashinta ya fadi duk da kashe kudi mai yawa a kayan aikin gona. Da dama daga cikinmu mun yi asara. Abin da ya kara muni, gwamnati ta ba da rangwame ga shigo da shinkafa. Shi ya sa muke shirin canzawa zuwa wasu kayan gona masu daraja domin ci gaba da kasancewa a wannan fanni. Mun gano cewa akasin shinkafa, samar da wake ya karu da kaso mai yawa a 2025, inda manoma suka samu kudin shiga fiye da na shinkafa a kowace hekta,” in ji shi.



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *