Babu wanda zai cire mu daga gasar kofin duniya — Iran

[ad_1]



Kasar Iran ta bayyana cewa babu wanda ya isa ya fitar da ita daga shiga gasar  kofin duniya da za a gudanar a ƙarshen wannan shekara, a matsayin martani ga gargaɗin Shugaba Donald Trump na cewa “rayuwarsu da tsaronsu” na iya kasancewa cikin haɗari a Amurka.

Tawagar ’yan ƙwallon ƙafar ta Iran ta kuma bayyana a wani saƙo da ta wallafa a shafukan sada zumunta ranar Alhamis cewa, bai kamata a bar Amurka ta ɗauki baƙuncin gasar ba, idan har ba za ta iya ba da tabbacin tsaron ƙungiyoyin da za su fafata ba.

Kalaman na Trump sun zo ne kwanaki biyu kacal bayan ya shaida wa shugaban FIFA, Gianni Infantino cewa ’yan wasan Iran na maraba duk da yaƙin da ake yi a Gabas ta Tsakiya.

“Ana maraba da Tawagar Kwallon Kafar Iran zuwa Gasar Cin Kofin Duniya, amma gaskiya ban yarda cewa ya dace su kasance a wurin ba, saboda kare rayuwarsu da tsaronsu,” in ji Trump a shafinsa na Gaskiya Social ranar Alhamis.

Tawagar Iran ta mayar da martani da cewa: “Gasar Cin Kofin Duniya wani babban taro ne na tarihi da ƙasa da ƙasa, kuma hukumar da ke gudanar da ita, ita ce FIFA — ba wani mutum ko ƙasa guda ba.

“Tawagar ƙasar Iran, tare da jajircewa da jerin gwanon nasarori da jaruman ’yan Iran suka samu, tana ɗaya daga cikin ƙungiyoyin farko da suka samu gurbin shiga wannan babbar gasa.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *