GORON JUMA’A

[ad_1]

Jama’a barkanmu da kasancewa a wannan rana ta juma’a, barkanmu da ibada, fatan kowa zai sha ruwa lafiya Allah ya karbi ibadunmu amin.    Kamar kowane mako shafin GORON JUMA’A shafi ne da ya saba karbar sakonnin gaishe-gaishenku zuwa ga ‘yan’uwa da abokan arziki, na kusa, da na nesa, har ma da wadanda aka dade ba a hadu ba.    A yau ma shafin na tafe da wasu sakonnin gaishe-gaishenku da kuka aiko mana kamar haka:

Sako daga Aminu I.B daga Gezawa:

Ina gaida mahaifina da mahaifiyata Karimatu, ina gaida kanne na Yusufu, isma’ilu, Lauratu, Aisha, Amina da yayana Zainuddin. Ina gaida abokaina na makarantar Malam  Kallamu me allo kamar su; Idirisu, Dahiru, Ubaidullahi, da dai saurans, fatan sun yi juma’a lafiya. Ina gaida ‘yan garinmu gabadaya, Allah kuma ya karbi ibadunmu, Amin.

Sako daga Umar Lawan Jihar Katsina:

Ina gaida masoyiyata abar kaunata, rabin raina Maryama, sako na gaba ina gaida Amir Yellow, da Hafiz a ci a zauna lafiya, ina gaida mainasara Kabeer dan fulani, ina gaida kannena da ‘yan’uwana da duk abokaina da suke ko’ina, duk ina gaishe su da fatan sun yi juma’a lafiya, da fatan kuma sun sha ruwa lafiya.

Sako daga Alaja Habiba Abdulmajid Jihar Kano:

Gaisuwar goron Juma’a zuwa ga mahaifiyata da kuma mahaifina, da fatan sun yi juma’a lafiya. Ina gaida kawayena kamar su; Mufida, takwarata Habiba, Zeenat, Munira, Amira, Fatima, Zainab Zeey Baby, Fa’iza, Amiran Mama, Zarah ‘Yar Chakaras, Salma Beauty, da dai sauransu da fatan kowacce ta yi juma’a lafiya.

Sako daga Aminu Shu’aibu Gidan Kaji Jahun:

Ina gaishe da yayana Buhari, Tijjani da Aisha da Zainab, Musa, da Yusuf, da abokina Audu. Ina gaida Awaisu, Abdulsalam, Yawale, da Kalis, da kanwata Shahida, da Baba Ado, da Baba Al’a, da Baba Sabo, da Halle, da Muzambilu, da Kamilu, da Gambo, da Baban kifi, da Sulaiman, Baban Yaya, da fatan sun yi juma’a lafiya, kuma za su sha ruwa lafiya.

Sako daga Habib Ahmad, Jihar Kano Unguwar Goron Dutse:

Ina gaishe da ‘Yan’uwana da ke garin Jos, irinsu Kalisat, Ummussalama, khadijatu, Auwal, Isuhu da sauransu. Sannan ina gaishe da Malamina Malam Muttaka da kuma Baballe abokina, ina gaishe da ‘Yan kungiyarmu ta ball, da fatan sun yi juma’a lafiya.

Sako daga Usman Bello Dikko daga Jihar Katsina:

Ina gaida Hajiyata, Mamana kenan Haj. Karima, kowa ya bar gida, gida ya barshi, sai mahaifina Alh. Bello, sai kannena da abokaina, irinsu, Yahaya ikon Allah, su Idris Shettima, Dan Maraya Musa, Lukman a zauna lafiya, ina gaida matata Hafsat Bebin bebi, ina gaida ‘Yan’uwanta da kannenta gabadaya, da fatan sun yi juma’a lafiya.

Sako daga Al’amin Shehu Jihar Kaduna:

Assalam. Ina gaida Mahaifana, ina gaida sauran ‘Yan’uwana, da abokan karatuna wadanda na jima ban gansu ba, da wadanda ma muke haduwa har yanzu, ina gaida Ummi da Mami, da Fati, ina gaida Abdulkareem, Idris dan baiwa, ina gaida, Alhaji Ali mazan duniya, ina gaida sauran al’umma gaba daya da fatan kowa yayi sallar juma’a lafiya.

Sako daga Gimbiya Aishat Sa’id Jihar Bauchi:

Gaisuwar goron juma’a zuwa ga ‘yan’uwa musulmi, da fatan sun yi juma’a lafiya. Ina gaida Zakiya da Haj.Mero, da Haj. Marka, da Haj. Sa’adatu me tuwon shinkafa, ina gaida Maryamu Isah, ina gaida Dijen Malan Aminu, da Hidayatu Ibrahim, ina gaida Abubakar Mustapha, Arabian kingboi, Muhd Kalgo, Mika’il Adam, da sauransu. Da fatan kowa ya yi Juma’a lafiya.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *