Iran Ta Kama Mutane Kusan 200 Kan Zargin Yi Wa Amurka Da Isra’ila Leƙen Asiri


Hukumomin Iran sun kama kusan mutane 200 da ake zargi da yi wa Amurka da Isra’ila leƙen asiri a lokacin da ake yaƙi tsakanin ƙasashen.

Wata ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama mai suna Human Rights Activists News Agency ta ce an kama mutane 195 a birnin Tehran da wasu birane, ciki har da Tabriz.

  • NNPC Ta Rage Farashin Fetur
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP, Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

A cewar ƙungiyar, an kama mutanen ne saboda zargin suna amfani da kafofin sada zumunta wajen aike hotuna da bidiyon hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai a Iran zuwa kafafen yaɗa labarai na duniya.

Rahotanni sun ce rundunar sojin Iran ma ta kama wasu mutane 10 da ake zargi da aika bidiyon hare-haren zuwa kafafen labarai na waje.

An kuma nuna su a talabijin suna amsa laifinsu.

Shugaban rundunar ’yansandan ƙasar, Ahmad Reza Radan, ya yi gargaɗin cewa duk wanda ya shiga zanga-zanga a wannan lokaci za a ɗauke shi a matsayin mai cin amanar ƙasa.

Hukumomin ƙasar sun kuma yi gargaɗi ga iyaye da su hana ’ya’yansu shiga zanga-zanga a ciki ko wajen ƙasar yayin da Iran ke ci gaba da gwabza yaƙi.

Wannan na zuwa ne a lokacin da rikicin da Amurka da Isra’ila ke yaƙi da Iran.



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *