Kwamitin Kolin JKS Da Majalisar Gudanarwa Ta Kasar Sin Sun Taya Tawagar Kasar Ta Wasannin Olympics Na Lokacin Hunturu Murna

[ad_1]

Kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS) da majalisar gudanarwar kasar sun aika sakon taya murna ga tawagar kasar Sin a gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu ta shekarar 2026 ta Milan-Cortina, suna masu yaba mata bisa samun sakamako mafi kyau a wasannin Olympics na lokacin hunturu da aka yi a ketare.

Tawagar ta samu yabo bisa yadda ta samarwa kasar Sin da al’ummarta lambobin zinare 5 da azurfa 4 da tagulla 6.

An kuma bukaci tawagar ta mayar da hankali wajen gina kasar Sin zuwa mai karfi a bangaren wasanni da ci gaba da kai wa sabbin matakai a fagen wasannin hunturu a duniya, ta yadda za ta karfafa da fadada nasarar kasar ta shigar da mutane miliyan 300 cikin wasannin lokacin hunturu. (FMM)

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *