Ƴan Bindiga Sun Buɗe Wuta Kan Makiyaya, Sun Jikkata Mutum 5 A Filato
[ad_1]
Wasu da ba a tantance ko su waye ba sun buɗe wuta kan makiyaya a ranar Lahadi a gidan mai na Conoil da ke kan titin Bukuru Expressway, a Ƙaramar Hukumar Jos ta Kudu dake Jihar Filato, inda mutane biyar suka jikkata.
Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) a jihar Plateau, Yusuf Babayo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce wata motar Peugeot J5 mai buɗaɗɗen baya da ke ɗauke da makiyaya takwas ta tsaya sayen mai ne a gidan man lokacin da wasu ƴan bindiga suka buɗe musu wuta. Ya ƙara da cewa makiyayan na dawowa ne daga Kasuwar Kara da ke Bukuru.
- Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Ƙungiyar Da Ke Safarar Makamai Tare Da Kama Mutane 3 A Filato
- MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
Mataimakin shugaban Kasuwar Kara, Dauda Adam Ciroma, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 7:30 na yamma, yana mai bayyana cewa jami’an ƴansanda sun gaggauta isa wurin tare da taimakawa wajen kai waɗanda suka jikkata asibiti. Ya ce dukkan waɗanda aka jikkata sun samu raunukan harbin bindiga da karayar ƙashi.
Babayo ya ce makiyayan an fara kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos (JUTH), amma daga bisani aka mayar da su Asibitin Potters Specialist da ke Jos sakamakon yajin aiki a asibitin gwamnati. Ya bayyana harin a matsayin wanda ba wani dalili, yana mai kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike tare da kama waɗanda suka aikata laifin. Ya kuma buƙaci mambobin ƙungiyar su kwantar da hankalinsu tare da kauce wa ɗaukar doka a hannunsu.
[ad_2]
Source link