Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti
[ad_1]
Wata babbar kotun Jihar Ekiti da ke zamanta a Ado Ekiti ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataye wani mai suna Stephen Adamu mai shekara 34 bisa laifin kashe ɗan uwansa.
An gurfanar da wanda ake tuhuma a gaban mai shari’a Adekunle Adeleye a ranar 31 ga watan Junairu, 2025, kan tuhumar kashe wani David Adamu, a sashi na 234 na dokar laifuka ta jihar Ekiti 2021.
Domin tabbatar da ƙarar sa, mai gabatar da ƙara Funmi Bello, ya kira shaidu shida da waɗanda ake ƙara da su gabatar da jawabi, da fom ɗin shaida da kuma wuƙa a matsayin nunin shaida.
Wanda ake tuhumar ya yi magana ta bakin Lauyansa, S.K Idowu, kuma bai kira wani shaida ba.
Da yake yanke hukuncin, mai shari’a Adeleye ya ce daga dukkan yanayin wannan shari’a, Stephen Adamu ya daɓa wa David Adamu wuƙa a wuya.
“Na sami wanda ake tuhuma da laifi kamar yadda ake tuhumarsa, wanda ake ƙara Stephen Adamu an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya,” in ji shi.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link