Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda

[ad_1]


Sheikh Ahmad Gumi, malamin addinin Musulunci mazaunin Kaduna, ya yabawa Tinubu kan afuwar da ya yi wa Maryam Sanda, wacce aka yanke mata hukuncin kisa a shekarar 2020 saboda kisan mijinta, Bilyaminu Bello, yana mai bayyana hakan a matsayin wani aikin rahama da ya yi daidai da ka’idojin Musulunci.

Shugaba Bola Tinubu ya fara yi wa Sanda afuwa tare da wasu fursunoni 174, ciki har da mutanen da aka samu da laifin safarar miyagun kwayoyi, garkuwa da mutane, da zamba. Wannan afuwar ta haifar da kalubale da cece-kuce a fadin kasar, wanda ya sa shugaban ya janye afuwar.

Amma kuma daga baya, bayan sake nazari aka mayar da hukuncin kisa na Sanda zuwa daurin shekaru 12 a gidan yari bisa abin da fadar shugaban kasa ta bayyana a matsayin “dalilai na tausayi ga yaranta.”

Da yake sharhi game da wannan batu a wani rubutu da ya yi a Facebook a ranar Alhamis, Sheikh Gumi ya ce, Sanda ta yi matukar nadama kuma ya tabbata ba halinta ba ne irin wannan mugun aiki face aikin shaiɗan ne ya yi sanadiyyar iftila’in, ba don son ranta ba ne.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *