‘Yansanda Sun Kama Matashi Mai Shekara 27 Kan Cin Zarafin Yarinyar Makwabta
[ad_1]
Hukumar ‘Yansanda ta Jihar Oyo ta kama wani mutum mai suna Olaitan Oloyede kan zargin cin zarafin karamin yarinya makwabta a yankin Oke-Alaro na birnin Ibadan.
PUNCH Metro ta samu labarin daga wata sanarwa da kakakin hukumar, Ayanlade Olayinka, ya fitar ranar Asabar da daddare, inda aka bayyana cewa lamarin ya faru a watan Oktoba.
- Manufar Yada-Zango Ba Tare Da Bukatar Biza Ba Ta Bunkasa Adadin Masu Shigowa Kasar Sin Domin Ziyara
- Bayan Shekara 9, Gwamnan Zamfara Ya Warware Matsalar Ɗaliban Jami’ar Crescent
Sanarwar ta ce, “Bincike ya nuna cewa wata yarinya mai shekaru takwas ta shaida wa mahaifinta cewa tana jin zafi a sassan jikinta na sirri kuma an yi mata fyade da makwabtar su mai shekaru 27, Olaitan Oloyede, a wani lokaci na watan Oktoba 2025.”
Bayan samun rahoton, hukumar ta bayyana cewa Rundunar ‘Yan Sanda ta Oke-Alaro ta fara bincike cikin gaggawa, wanda ya kai ga kama wanda ake zargi.
Sanarwar ta kara da cewa, “Masu bincike daga Rundunar Oke-Alaro, karkashin jagorancin DPO, sun kai yarinyar asibiti don duba lafiyarta, samun magani da kuma tallafi, inda take karbar kulawa da goyon bayan da ya dace.”
A halin yanzu, wanda ake zargi yana cikin tsarewa bisa doka kuma yana ba da hadin kai ga bincike, wanda ya baiwa ‘yan sanda damar ci gaba da gudanar da binciken.
Sanarwar ta kuma nuna cewa Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Oyo, Femi Haruna, ya nuna rashin jin dadinsa sosai kan lamarin, tare da yaba wa shugabancin IGP Kayode Egbetokun kan jagorancinsa wajen inganta bincike bisa sirri da kare masu rauni.
“CP Haruna ya umarci a mika lamarin zuwa State CID Gender Desk’ domin bincike cikin sirri da tabbatar da gudanar da shi yadda ya kamata,” in ji sanarwar.
Hukumar ta sake jaddada cewa ba za ta lamunce kowanne irin cin zarafi ko tashin hankali kan yara ko jinsi ba, tare da gargadin iyaye, da masu kula da yara da al’umma da su rika kai rahoton duk wani zargin cin zarafi ga mafi kusa ofishin ‘yansanda.
Har ila yau, hukumar ta tabbatar da ci gaba da yaki da laifuka masu karfi a jihar Oyo da tabbatar da adalci ga dukkan wadanda abin ya shafa.
Kamanin kwanaki bakwai kacal kafin wannan kama, hukumar ta bayyana kama wani mutum kan wani laifi makamancin haka da ya shafi yarinya mai shekaru 17.
‘Yansanda sun bayyana wannan kama a matsayin wata nasara ta aikin su wajen kare mazauna jihar.
[ad_2]
Source link