’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

[ad_1]



Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta kama matashin nan da ake zargi da kashe makwabciyarsa a unguwar Shuwari II, a garin Maiduguri babban birnin jihar, ta hanyar daba mata wuka.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:00 na dare a ranar Talata.

Ya ce ana zargin matashin ne mai shekaru 17 da aka fi sani da Amir, wanda makanike ne da kashe matar ta hanyar daba mata wuka.

Wani makwabcin wajen ya shaida cewa ana zargin matashin ne da shiga gidan ta hanyar tsallake katanga bayan ya jira ragowar mutanen gidan sun shiga ciki.

A cewar majiyar, matashin ya ɗauki wuƙa ya daba wa matar gidan, wadda ba a bayyana sunanta ba, a ƙirji da wuya, sannan ya tafi da wayarta da na’urar cajin hannu (power bank).

Majiyar ta ƙara da cewa bayan aikata laifin, wanda ake zargin ya koma gidansu ya wanke tufafinsa da kayan da ya yi amfani da su domin kauce wa bin sahunsa.

Rahotanni sun ce ƙanwar mijin wadda aka kashe ce ta fara sanar da jama’a bayan ta ji ihun matar tana neman taimako.

Lokacin da ta fito ta duba, sai ta ga wanda ake zargin yana gudu ya koma gidansu.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa jami’an ’yan sanda sun kama matashin da misalin ƙarfe 2:30 na rana.

Sai dai kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, bai samu damar yin ƙarin bayani ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *