Boko Haram Sun Sake Kai Hari Kan Wani Sansanin Sojoji A Borno

[ad_1]

Wasu da ake zargin mayaƙan ƙungiyar Boko Haram ne sun kai hari kan wani sansanin sojoji da ke Ajilari, wanda yake a wajen birnin Maiduguri, babban birnin jihar Borno.
Rahotanni sun ce harin na Ajilari ya faru ne a lokaci guda da wani hari a garin Baga, inda majiyoyi suka bayyana cewa ‘yan ta’addan sun gwabza yaki da sojoji a sansanin sojojin Baga.
  1. Binciken CGTN: Shawarar Inganta Wayewar Kai A Duniya Ta Kasar Sin Na Kawo Zaman Lumana Ga Duniya Mai Cike Da Hargitsi
  • Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Birnin Paris
Majiyoyi sun shaida wa wakilin jaridar Daily Trust cewa, maharan sun kutsa cikin yankin ne da misalin karfe 12:30 na dare.
Sai dai kuma, martani cikin gaggawa daga rundunar haɗin gwiwa ta sojoji, ‘yansanda, rundunar sa-kai ta CJTF, da kuma sojojin sama ya tilasta wa maharan ja da baya.
Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa jami’an tsaro sun riga sun ɗauki matakan da suka dace domin shawo kan lamarin.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *