’Yan sanda za su ci gaba da aiwatar da dokar motoci masu gilashi mai duhu

[ad_1]



Shugaban ’Yan Sandan Najeriya ya bayyana cewa za a ci gaba da aiwatar da dokar izinin amfani da gilashi mota mai duhu da aka dakatar na ɗan lokaci.

Ya jaddada cewa babu wata kotu da ta hana aiwatar da tsarin, wanda za a fara ne daga ranar 2 ga Janairu, 2026.

Ya ce Hukumar ta yanke wannan shawara ne bayan ta lura da sabbin matsalolin tsaro da kuma buƙatar kare rayukan ’yan ƙasa.

Kakakin rundunar, Benjamin Hundeyin, ya sanar da cewa an samu mummunan tashin hankali na ƙaruwar laifuka ta hanyar amfani da motocin da aka saka gilashi mai duhu ba tare da izini ba.

Ya ce, “Rundunar ’Yan Sandan Najeriya na sanar da jama’a cewa za a ci gaba da aiwatar da dokar izinin gilashin duhu yayin da ake jiran hukuncin karshe na shari’ar da ke gaban kotu.

“Wannan mataki ya biyo bayan nazari mai zurfi kan sabbin matsalolin tsaro da kuma bukatar kare rayukan ’yan ƙasa.

“Ya kamata a fayyace cewa a kowane lokaci ba kotu ta hana Rundunar ’Yan Sandan Najeriya aiwatar da dokar da ta shafi amfani da gilashin duhu a kan motocin.

“Duk da haka, a cikin ruhin daukar alhakin, gaskiya da sauƙaƙa wa jama’a, Rundunar ta dakatar da aiwatar da dokar na ɗan lokaci domin ba wa direbobi damar daidaita takardunsu da kammala rajista ba tare da matsin lamba ba.

“Sabbin abubuwa, duk da haka, sun nuna tashin hankali na laifuka da ake aikatawa ta amfani da motocin da aka saka gilashin duhu ba tare da izini ba.

“Wasu mutane da kungiyoyin laifuka sun yi amfani da wannan gibi wajen boye kansu da kuma sauƙaƙa aikata laifuka daga fashi da makami zuwa garkuwa da mutane da sauran laifukan tashin hankali.

“Saboda haka, Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta ga ya zama dole kuma gaggawa ta ci gaba da cikakken aiwatar da dokar a matsayin matakin kariya ga al’ummominmu.

“Saboda haka, aiwatar da izinin gilashin duhu zai ci gaba daga 2 ga Janairu, 2026.

“Babban Sufeto Janar na ’Yan Sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya tabbatar wa jama’a cewa aiwatar da dokar zai gudana cikin kwarewa, girmama ’yancin ’yan ƙasa, da kuma bin dokokin da suka dace.”

Hundeyin ya bayyana cewa direbobi da ke bukatar izinin gilashin duhu ana ƙarfafa su su nemi ta hanyar da aka amince da ita kuma su tabbatar da cewa motocinsu sun dace da ka’idojin doka.

Ya kara da cewa Rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen kare jama’a da tabbatar da bin doka, tare da yin aiki kafada da kafada da dukkan masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaron Najeriya.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *