’Yan Bindiga Sun Kai Hari Tare Da Kashe Ɗan Kasuwa A Kano

[ad_1]

’Yan bindiga sun kai hari garin Tiga da le ƙaramar hukumar Bebeji a daren ranar Litinin a Jihar Kano.

Sun kashe wani fitaccen ɗan kasuwa, Alhaji Habibu Mai Shago, a cikin shagonsa.

  • Da Gaske Ne Wasu Jami’ai 16 Sun Yi Yunƙurin Kifar Da Gwamnatin Tinubu — DHQ
  • Dalilan Da Suka Sa Na Sauya Sheƙa Zuwa Jami’yyar APC – Gwamnan Kano

Har ila yau, sun sace kayayyaki sannan suka tsere.

Harin ya jefa mazauna garin cikin tsoro, inda suka nuna damuwa game da ƙaruwar hare-haren a ƙauyukan.

Wani masanin harkokin tsaro, mai suna DanKatsina50 ne, ya wallafa labarin a shafinsa na X.

Al’ummar yankin sun bayyana Alhaji Habibu Mai Shago a matsayin mutumin kirki, mai aiki tuƙuru kuma mai son zaman lafiya.

Har yanzu, hukumomi a Jihar Kano ba su fitar da wata sanarwa game da harin ba.

Mazauna garin sun roƙi hukumomin tsaro da su tura ƙarin jami’ai domin kare su daga hare-haren ‘yan bindiga.

A baya-bayan nan dai, yankunan da ke maƙwabtaka da jihar Katsina na fuskantar hare-haren ‘yan bindiga, lamarin da ya sanya gwamnatin Kano da ta Tarayya tura jami’an tsaro, domin kare al’umma.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *