’Yan bindiga sun bude wa masu sallah a masallaci wuta a Katsina

[ad_1]



Mutane da dama ne suka mutu sannan wasu masu yawa suka jikkata sakamakon wani hari da ’yan bindiga suka kai kan masallatan da ke tsaka da sallah a jihar Katsina.

Rahotanni sun ce an kai harin ne a kauyen Unguwar Mantau da ke karamar hukumar Malumfashi a jihar.

Mazauna yankin sun ce an kai harin ne lokacin da mutanen garin ke tsaka da sallar Asuba ta ranar Talata.

Aminiya ta gano cewa harin na ramuwar gayya ne biyo bayan wanda mazauna yankin suka kai kan ’yan ta’addan, wanda ya kai ga kashe da dama daga cikinsu sannan aka kwace musu makamai da babura.

Wani mazaunin yankin da bai amince a bayyana sunansa ba ya ce ana fargabar adadin wadanda suka mutu zai iya haura na farkon kasancewar an garzaya da wasu da suka samu raunuka zuwa asibiti a cikin mummunan yanayi.

“Mun samu labarin adadin wadanda suka mutu yanzu sun haura 22,” in ji shi.

Da yake tabbatar da harin, Kwamishinan Tsaro da Al’amuran Cikin Gida, Dr Nasir Mu’azu, ya ce sun samu labarin ’yan ta’addan harin ramuwar gayya suka kai.

“Musulmai na sallar Asuba a cikin masallaci lokacin da ’yan ta’addan suka bude musu wuta a cikin masallaci,” in ji Kwamishinan.

Ya kuma ce tuni gwamnatin jihar ta tura karin jami’an tsaro yankin domin kwantar da tarzoma.

Ya kara da cewa, “Harin na ramuwar gayya ne kan kare kansu da mutanen yankin suka yi kwanaki biyu kafin faruwar shi. Mutanen sun yi kwanton bauna ga ’yan ta’addan, inda suka kashe da dama daga cikinsu sannan suka kwato wasu da aka yi garkuwa da su daga kauyen Ruwan Sanyi, suka kwato babura uku da bindiga kirar AK-47 guda biyu.

“Tuni mun tura karin jami’an tsaro zuwa yankin domin bayar da tsaro. Kuma a matsayinmu na gwamnati, muna jinjinawa jajircewar mutanen Unguwar Mantau a kan ’yan ta’adda, kuma za mu ci gaba da iya bakin kokarinmu wajen ganin mun ga bayan maharan,” in ji Nasir.

Galibi dai a kan samu karuwar hare-haren ’yan ta’adda a yankuna da dama na jihar ta Katsina, musamman da damina lokacin da manoma suke aikin gona.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *