Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas

[ad_1]

Gwamnatin Tarayya ta fitar da gargaɗin tsaro ga ’yan Nijeriya da ke zaune a Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma ƙasashen Tekun Fasha maƙwabta, sakamakon ƙarin tashin hankali da hare-haren soji a yankin.

A cikin wata sanarwar manema labarai da aka fitar ranar Asabar, mai ɗauke da sa hannun kakakin Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, gwamnati ta ce tana “sa ido sosai kan halin da ake ciki mai sauyawa da rikitarwa a Gabas ta Tsakiya, musamman dangane da hare-haren soji da ake zargin Isra’ila da Amurka sun kai kan wasu wurare a Jamhuriyar Musulunci ta Iran, da kuma martanin da Iran ta mayar kan wasu wurare a wasu ƙasashen Tekun Fasha.”

  • Yaƙin Iran Zai Asassa Tashin Farashin Man Fetur A Nijeriya
  • Kamfanin Matatar Man Fetur Na Dangote Ya Rage Farashin Mai Zuwa ₦774

Dangane da ƙaruwar tashin hankalin, ma’aikatar ta shawarci ’yan Nijeriya da ke yankunan da abin ya shafa da su yi taka-tsantsan matuƙa.

“An shawarci dukkan ’yan Nijeriya da ke Iran da ƙasashen Tekun Fasha da abin ya shafa da su kasance cikin tsananin lura da kuma kula da muhallinsu a kowane lokaci. Su guji wuraren da aka sani a matsayin muhimman cibiyoyi na dabarun soja ko na gwamnati, domin irin waɗannan wurare na iya zama wuraren tashin hankali,” in ji sanarwar.

Ta kuma buƙaci ’yan ƙasa da su taƙaita zirga-zirgarsu, inda ta ce, “Ana ba da shawara sosai ga ’yan Nijeriya da su taƙaita duk wata tafiya ko motsi da ba dole ba a cikin ƙasar har sai yanayin tsaro ya ƙara bayyana kuma ya daidaita. A guji manyan taruka da zanga-zangar jama’a.”

Gwamnatin ta kuma umarci ’yan Nijeriya da su bi umarnin hukumomin ƙasashen da suke zaune.

“An shawarci ’yan ƙasa da su bi dukkan umarni da ƙa’idojin tsaro da hukumomin ƙasar da suke ciki suka bayar domin kare lafiyarsu. Ku tuna cewa haɗin kai da jami’an tsaro na ƙasar yana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da tsaro,” in ji sanarwar.

Dangane da sadarwa, ma’aikatar ta bayyana cewa Ofishin Jakadancin Nijeriya da ke Tehran da kuma ofisoshin jakadancin da ke ƙasashen Tekun Fasha maƙwabta, ciki har da Ƙatar, Bahrain, Kuwait, Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da Saudiyya, “na cikin shirin ko-ta-kwana domin bayar da duk wani taimakon jakadanci da kuma sauƙaƙa sadarwa.”

Ma’aikatar ta tabbatar da cewa “tsaro da jin daɗin ’yan Nijeriya da ke ƙasashen waje su ne a sahun gaba na fifikon Gwamnatin Tarayya,” tare da ƙara da cewa za ta ci gaba da tantance halin da ake ciki tare da bayar da ƙarin bayani idan ya zama dole.

Haka kuma, gwamnatin ta yi kira ga ɓangarorin da ke cikin rikicin “da su rage tashin hankalin ta hanyar komawa kan teburin tattaunawa domin muradun zaman lafiya da zaman tare na duniya baki ɗaya.”

Wannan gargaɗin ya biyo bayan jerin hare-haren da United States da Israel suka kai ranar Asabar kan wasu wurare a biranen Iran, lamarin da ya haddasa fashe-fashe da watsuwar hayaƙi a babban birnin ƙasar, Tehran.

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce manufar Washington ita ce “kawar da barazanar gaggawa” daga Iran, yayin da Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya bayyana matakin a matsayin “harin kariya kafin aukuwar hari.”

A cikin wani saƙon bidiyo, Trump ya ce, “Sojojin Amurka sun fara manyan hare-haren yaƙi a Iran,” tare da ƙara da cewa, “Za mu lalata tashar makamansu tare da rushe masana’antar ƙera makaman Nukiliyarsu baki ɗaya. Za a shafe su gabaki ɗaya. Za mu murƙushe rundunar ruwansu.”

Ƙungiyar African Union ta bayyana matuƙar damuwa kan ƙara tsanantar rikicin, tana gargaɗin cewa hakan na barazana ga zaman lafiyar duniya, yayin da European Union ma ta mayar da martani.

Shugaban European Council, António Costa, ya ce, “Abubuwan da ke faruwa a Iran na matuƙar tayar da hankali. Muna ci gaba da kasancewa cikin tuntuɓa ta kusa da abokan hulɗarmu a yankin.”

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *