Umar FK ya fice daga PDP zuwa APC da magoya bayansa a Gombe

[ad_1]



Siyasar Jihar Gombe ta ƙara ɗaukar zafi yayin da fitaccen ɗan siyasar nan, Umar Faruk FK, ya fice daga jam’iyyar PDP tare da dimbin magoya bayansa, tare da komawa APC.

FK, ya bayyana cewa PDP ta gaza bayar da shugabanci nagari a jihar, shi ya sa ya yanke shawarar barin ta.

Ya ce ya mara wa Gwamna Inuwa Yahaya baya bisa ayyukan ci gaba da ya ke gudanarwa.

“Marar kishin Gombe ne kawai ba zai ga nasarorin da gwamnatin Inuwa Yahaya ke samu ba,” in ji Umar FK.

Ya ƙara da cewa shi da magoya bayansa za su mara wa gwamnan baya a shirin neman kujerar Sanatan Gombe Arewa a 2027.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, da shugaban APC a Ƙaramar Hukumar, Alhaji Abubakar Danladi, sun tarbi FK cikin farin ciki, inda suka ce dawowarsa babbar nasara ce da za ta ƙara APC ƙarfi a jihar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *