Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

[ad_1]

Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a dawo da babban daraktan gidan talabijin na Nijeriya (NTA), Salihu Abdullahi Dembos, wanda aka dakatar bayan wasu sauye-sauye da aka samu a shugabancin gidan.

Shugaba Tinubu ne ya nada Dembos a matsayin babban darakta na gidan talabijin a watan Oktoban 2023.

Amma a yanzu zai dawo ya kammala wa’adinsa na ragowar shekaru uku.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar, shugaban ya kuma umarci da a maido da babban daraktan yada labarai, Mista Ayo Adewuyi ya kammala wa’adinsa na ragowar shekaru uku, wanda zai kare a shekarar 2027.

Shugaba Tinubu ne ya nada Adewuyi a shekarar 2024.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *