Tawagar Gwamna ta gana da Sarki Sanusi II

[ad_1]



’Yan sa’o’i kaɗan bayan karɓar baƙuncin manyan jami’an gwamnati a taron buɗe baki (Iftar) a fadarsa, Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya gudanar da wata ganawar sirri da wata tawaga daga Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Lamarin dai ya rura wutar hasashen matsayar jihar kan taƙaddamar sarautar da ake yi.

Kakakin Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya tabbatar da ganawar a wani saƙo da ya wallafa a Facebook da safiyar ranar Laraba, inda ya ce an gudanar da ganawar ne a fadar Gidan Rumfa.

Ya bayyana cewa, waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Sakataren Gwamnatin Jiha (SSG), Umar Ibrahim, Shugaban Ma’aikatan Gwamna, Sulaiman Wali Sani, da kuma shi kansa.

Dawakin Tofa ya rubuta cewa: “Jim kaɗan bayan buɗe baki a Fadar Sarki, tawagar Gwamnan ta yi wata ganawar sirri da Mai Martaba.”

Wannan na zuwa ne yayin da birnin Kano ke shirye-shiryen shagulgulan ƙaramar Sallah na Idil-Fitr da kuma gagarumin Hawan Sallah na tarihi.

Hawan Sallar, wanda tsohon al’ada ne da aka daɗe ana yi, ya shiga yanayin rashin tabbas biyo bayan maganganu masu karo da juna daga jami’an gwamnati kan ko za a yi shi a wannan shekarar, ganin yadda har yanzu akwai taƙaddamar shari’a tsakanin Sanusi II da Aminu Ado Bayero da ba a warware ba.

Duk da cewa Gwamna Yusuf ya mayar da Sanusi II kan mulki a shekarar 2024, Bayero na ci gaba da ƙalubalantar tsige shi a kotu, wanda hakan ya sa batun sarautar ke cikin ruɗani.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *