Sule Lamiɗo na neman takarar Shugaban PDP na Ƙasa

[ad_1]



Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Alhaji Sule Lamiɗo ya bayyana kudirinsa na sayen tikitin neman zama sabon Shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa.

Tsohon ministan ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa kudurinsa na ganin an dawo da martabar dimokuraɗiyya da kuma farfaɗo da darajar jam’iyyar yadda take da, ba zai taɓa yankewa ba.

Tsohon gwamnan na Jigawa na cikin sahun farko na wadanda aka kafa jam’iyyar ta PDP da su a Nijeriya, kuma na gaba-gaba a takarar neman zama sabon shugaban jam’iyyar ta PDP daga Arewa maso Yamma.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *