Sojoji Sun Ƙwato Shanun Sata A Filato

[ad_1]

Sojojin Operation Safe Haven sun ƙwato wasu shanu da aka sace a Jihar Filato, bayan wani samame da suka gudanar a ƙaramar hukumar Riyom.

Wannan na cikin wani saƙo da masanin harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya wallafa a shafinsa na X.

  • CAF Ta Soke Nasarar Senegal, Ta Ayyaṇa Morocco A Matsayin Zakarar AFCON Ta 2025
  • Madrid Da PSG Na Shirin Sayen Osimhen

Rahoton ya ce sojojin Sashe na 6 da ke Makera sun samu sahihan bayanai da misalin ƙarfe 7:20 na safiyar ranar Litinin, game da motsin wasu shanu da ake zargin an sace su a kusa da ƙauyen Tahoos.

Nan take sojojin suka kai samame yankin, inda suka gano shanu shida da ɓarayin suka bari bayan sun gudu da ganin jami’an tsaro.

Daga baya an miƙa shanun ga mai su.

Majiyoyin tsaro sun ce sojoji na ci gaba da sintiri a yankin domin hana sake faruwar irin wannan laifi da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *