Sojoji sun kama mai yi wa Boko Haram safarar man fetur a Borno
[ad_1]
Dakarun Operation Haɗin Kai su kama wani mutum da ake zargi yana kai wa Boko Haram man fetur a Jihar Borno.
Wanda aka kama, mai suna Thomas James, mai shekaru 54, an cafke shi ne ranar 23 ga watan Satumba a kusa da sansanin Forward Operating Base da ke Ngwom.
An same shi da kwalabe 23 na man fetur da ya ɓoye cikin jaka a lokacin da yake tafiya daga Maiduguri zuwa Gamboru Ngala.
Bincike ya gano cewa yana yi wa Boko Haram safarar man fetur, sai dai wannan karon an yi nasarar kama shi.
Wanda dai ba shi ne karon farko da ake kama waɗanda ke da alaƙa da Boko Haram ba.
A baya jami’an tsaro a Jihar Borno, sun sha kama masu yi wa ’yan ta’addan safarar makamai, abinci da sauransu.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link